< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Le méchant se sauve quand personne ne le poursuit, mais les justes sont pleins d’assurance comme un jeune lion.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
À cause de l’iniquité d’un pays, ses princes sont nombreux; mais, par un homme intelligent qui a de la connaissance, la stabilité se prolonge.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
L’homme pauvre qui opprime les misérables est une pluie violente qui [ne laisse] point de pain.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Ceux qui abandonnent la loi louent les méchants, mais ceux qui gardent la loi leur font la guerre.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Les hommes adonnés au mal ne comprennent pas le juste jugement, mais ceux qui cherchent l’Éternel comprennent tout.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Mieux vaut le pauvre qui marche dans son intégrité, que l’homme pervers dans ses doubles voies, bien qu’il soit riche.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Qui garde la loi est un fils intelligent; mais le compagnon des débauchés fait honte à son père.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
Celui qui augmente son bien par l’intérêt et l’usure, l’amasse pour celui qui est bon pour les misérables.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
Qui détourne son oreille pour ne pas écouter la loi, sa prière même est une abomination.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Celui qui égare les hommes droits sur un mauvais chemin tombera lui-même dans la fosse qu’il aura creusée; mais les hommes intègres hériteront le bien.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
L’homme riche est sage à ses yeux, mais le pauvre qui est intelligent le sonde.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Quand les justes se réjouissent il y a beaucoup de gloire; mais quand les méchants se lèvent, les hommes se cachent.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
Celui qui cache ses transgressions ne prospérera point, mais celui qui les confesse et les abandonne obtiendra miséricorde.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Bienheureux l’homme qui craint continuellement; mais celui qui endurcit son cœur tombera dans le malheur.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Un lion rugissant et un ours à la poursuite de sa proie, c’est le dominateur méchant d’un peuple pauvre.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Le prince privé d’intelligence opprime beaucoup, [mais] celui qui hait le gain déshonnête prolongera [ses] jours.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
L’homme chargé du sang d’une âme fuira jusqu’à la fosse, … qu’on ne le retienne pas!
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Qui marche dans l’intégrité sera sauvé, mais qui suit tortueusement deux voies tombera une fois pour toutes.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
Qui laboure sa terre sera rassasié de pain, mais qui court après les fainéants sera rassasié de pauvreté.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
L’homme fidèle abonde en bénédictions, mais celui qui a hâte de s’enrichir ne demeurera pas innocent.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Faire acception des personnes n’est pas bien; même pour un morceau de pain un homme commettra une transgression.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
L’homme qui a l’œil mauvais se hâte pour avoir des richesses, et il ne sait pas que la disette viendra sur lui.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
Celui qui reprend un homme trouvera la faveur dans la suite, plutôt que celui qui flatte de la langue.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Qui dépouille son père et sa mère, et dit: Ce n’est point une transgression, celui-là est compagnon du destructeur.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
Celui qui a l’âme altière excite la querelle; mais qui se confie en l’Éternel sera engraissé.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
Qui se confie en son propre cœur est un sot; mais qui marche dans la sagesse, celui-là sera délivré.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
Qui donne au pauvre ne manquera de rien, mais qui détourne les yeux sera comblé de malédictions.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Quand les méchants se lèvent, les hommes se cachent; mais quand ils périssent, les justes se multiplient.

< Karin Magana 28 >