< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Wicked [people] run away [even] when no one is pursuing them, but righteous/good [people are not afraid]; they are as brave as lions.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
When [the people of] a nation sin, they will have one ruler after another; but when their leaders are wise and have good sense, their government will last for a long time.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
A poor person who oppresses [other] poor [people] is [like] [MET] a very heavy/hard rain that [destroys the crops], with the result that there is no food [for people to eat].
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Those who reject/disobey [God’s] laws always speak well of wicked [people]; but those who obey [God’s] laws [always] oppose what wicked people do.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Evil people do not understand what it means to act justly, but those who try to obey/worship Yahweh understand that very well.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
It is better to be honest [even] though you are poor than to be dishonest [even] though you are rich.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Young people who obey the laws are wise [IDM]; parents whose children associate with those who (carouse/go to wild parties) are humiliated/disgraced because of what their children do.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
When people become very rich by charging very high interest [DOU], their money will [eventually] go to someone who does kind things for the poor.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
If people do not obey [MTY] [God’s] laws, [God] (detests their prayers/considers that their prayers stink).
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Those who cause honest/good [people] to do what is evil will fall into their own pits/traps, but good things will happen to those who (are innocent/have not done what is wrong).
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
[Many] rich people think that they are wise, but poor people who have good sense will find out whether rich people really are wise or not.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
When righteous/good [people] (succeed/win [elections]), everyone (celebrates/is happy); but when wicked [people win], everyone hides [because they are afraid of what the wicked people will do].
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
Those who refuse to confess/admit their sins will not prosper, but [God] acts mercifully/kindly toward those who confess their sins and turn away from their sinful behavior.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
[God] is pleased with those who always revere him, but those who are stubborn [IDM] will experience disasters.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Wicked people who [mistreat] poor people whom they rule are [as dangerous to them as] [SIM] a lion roaring [at them] or a bear springing up [to attack them].
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
Rulers who do not have good sense cruelly oppress [the people they rule], but rulers who do not want to become rich by cheating/deceiving [people] will live (OR, rule) for a long time.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
Those who are guilty of murdering [MTY] another person will (be fugitives/keep running away) until they die; do not help them to escape.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Those who [continually] do what is right will be safe/protected, but those who are dishonest will [suddenly] be ruined.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
Farmers who work [hard] in their fields will [produce good crops and always] have plenty of food [to eat], but those who spend all their time (on useless projects/doing things that do not benefit anyone) will become very poor.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
[God] will greatly bless those who (are trustworthy/always do what they say that they will do), but he will certainly punish [LIT] those who try to become rich quickly.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
It is not good [for judges] to decide matters unfairly/unjustly, but [some] people will do what is wrong [even] if they receive [only] a very small bribe [HYP] [for doing it].
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
Selfish people [IDM] are very eager to become rich quickly; they do not realize that they will [soon] become poor.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
Those who rebuke someone will be appreciated/thanked more than those who [say nice things to others merely] to (flatter them/cause them to feel good).
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Anyone who steals things from his father or his mother and says “That is not sinful” is as bad as a bandit.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
Greedy people cause trouble/strife; those who trust in Yahweh will prosper [IDM].
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
Those who believe that what they think [is always right] are foolish; those who act wisely will (escape danger/be safe).
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
Those who give things to poor [people] will not become poor, but many [people] will curse those who refuse to help [IDM] poor people.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
When wicked [people] become rulers, people hide [because they are afraid of what those wicked people will do]; but when wicked people are no longer rulers, good/righteous [people will] become the rulers.

< Karin Magana 28 >