< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
The lawless, fleeth when no man pursueth, but, the righteous, like a lion, are confident.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
For the transgressions of a land, many are the rulers thereof, but, under an intelligent and discerning man, stability is prolonged.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
A poor man, who oppresseth the helpless, [is like] a rain beating down, leaving no food.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
They who forsake instruction, praise one who is lawless, while, they who keep instruction, are at strife with them.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Wicked men, consider not justice, but, they who seek Yahweh, consider everything.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Better a poor man walking in his integrity, than one who is crooked—turning two ways, though, he, be rich.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
He that keepeth instruction, is a son with discernment, but, a companion of squanderers, bringeth shame to his father.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
He that increaseth his substance by interest and profit, for one ready to favour the poor, doth gather it.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
He that turneth away his ear from hearing instruction, even his prayer, is an abomination.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
He that misguideth the upright into a hurtful way! into his own pit, he himself, shall fall, but, men of integrity, shall inherit good.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
Wise in his own eyes, is the man that is rich, but, a poor man of discernment, searcheth him out.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
In the exulting of the righteous, there is great glorying, but, when the lawless arise, a man must be sought for.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
He that covereth his transgressions, shall not prosper, but, he that confesseth and forsaketh, shall find compassion.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
How happy the man who is ever circumspect, whereas, he that hardeneth his heart, shall fall into calamity.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
A growling lion, and a ranging bear, is a lawless ruler, over a poor people.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
A leader, may lack intelligence, yet abound in oppressions, The hater of greed, shall lengthen out days.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
A man oppressed with a person’s blood, unto a pit, shall flee, let them not hold him back.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
He that walketh with integrity, shall be saved, but, he that is crooked, turning two ways, shall fall in one.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
He that tilleth his ground, shall have plenty of bread, but, he that pursueth empty-heads, shall have plenty of poverty.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
A man of fidelity, aboundeth in blessings, but, one hasting to be rich, shall not be held innocent.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
To take note of faces [in judgment], is not good, and, for a bit of bread, a man will transgress.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
A man, hasting to be rich, hath an evil eye, and knoweth not when want may overtake him.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
He that reproveth a man, shall, afterwards, find more, favour, than he that useth a flattering tongue.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
He that robbeth his father or his mother, and saith, It is no transgression, companion, is he to one who wasteth.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
The ambitious in soul, stirreth up strife, but, he that trusteth in Yahweh, shall be enriched.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
He that trusteth his own heart, the same, is a dullard, but, he that walketh wisely, the same, shall be delivered.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
One who giveth to the poor, shall have no want, but, he that hideth his eyes, shall receive many a curse.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
When lawless men rise, a common man will hide himself, but, when they perish, righteous men multiply.

< Karin Magana 28 >