< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Every wicked fleeth when no man pursueth; but the righteous are like the confident young lion.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
When there is transgression in a land, it hath many for its princes; but under a man of understanding and knowledge [its] prosperity will long continue.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
A poor man that oppresseth the indigent is like a sweeping rain which bringeth no bread.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
They that forsake the law praise the wicked; but such as observe the law contend with them.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Bad men understand not justice; but they that seek the Lord understand all things.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Better is the poor that walketh in his integrity, than he that is perverse in his ways, though he be rich.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
Whoso keepeth the law is an intelligent son; but he that is a companion of gluttons bringeth dishonor on his father.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
He that increaseth his wealth by interest and usury will gather it for him that will be kind to the poor.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
When one turneth away his ear so as not to listen to the law, even his prayer becometh an abomination.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
Whoso causeth the upright to go astray on an evil way, will surely fall into his own ditch; but the men of integrity will inherit what is good.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
The rich man is wise in his own eyes; but the indigent that hath understanding can search him through.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
When the righteous exult, there is great splendor; but when the wicked rise up, a man hath to be sought for.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
He that concealeth his transgressions will not prosper; but whoso confesseth and forsaketh them will obtain mercy.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Happy is the man that always dreadeth [to do evil]; but he that hardeneth his heart will fall into unhappiness.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
As a roaring lion, and a greedy bear, so is a wicked ruler over an indigent people.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
The prince that is void of understanding is also a great oppressor; [but] he that hateth unjust gain will prolong his days.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
A man oppressed by the load of having shed human blood will flee even to the pit: let no man hold him.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
Whoso walketh in integrity will be saved; but he that walketh perversely on two paths, will fall on one.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
He that tilleth his ground will have plenty of bread; but he that runneth after idle persons will have enough of poverty.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
A faithful man will abound with blessings; but he that maketh haste to be rich will not go unpunished.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
To have respect to persons is not good; because even for a piece of bread will a man transgress.
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
He that is eager for wealth is a man of an evil eye, and he knoweth not that want will come upon him.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
He that reproveth a man after [my example] will obtain more grace than he that flattereth with the tongue.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
Whoso robbeth his father or his mother, and saith, it is no transgression, —the same is a companion of a destroyer.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
He that hath an insatiable desire stirreth up strife: but he that putteth his trust in the Lord will be abundantly gratified.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
He that trusteth in his own sense is a fool; but whoso walketh in wisdom, will ever escape.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
He that giveth unto the poor will not have any want; but he that hideth his eyes will have an abundance of curses.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
When the wicked rise, men conceal themselves; but when they perish, the righteous increase.

< Karin Magana 28 >