< Karin Magana 27 >
1 Kada ka yi fariya a kan gobe gama ba san abin da ranar za tă kawo ba.
Kik isungri kuom kiny, nikech ok ingʼeyo gima odiechiengʼ nyalo kelo.
2 Ka bar wani ya yabe ka, ba kai kanka ba; wani dabam, ba leɓunanka ba.
We ngʼat moro ema opaki, to ok dhogi iwuon; ngʼato machielo, to ok lewi iwuon.
3 Dutse yana da nauyi yashi kuma wahala ce, amma tsokanar wawa ta fi su duka nauyi.
Kidi pek to kuoyo bende pek, to chandruok ma ngʼat mofuwo kelo pek moloyo gik moko ariyogo.
4 Fushi mugun abu ne mai hallakarwa, amma wa zai iya tsaya a gaban kishi?
Mirima kwiny to gero pek moloyo, to en ngʼa manyalo chomore gi nyiego?
5 Gara tsawatawar da ake yi a fili da ƙaunar da ake yi a ɓoye.
Kwero ngʼato ratiro ber moloyo hera mopandi.
6 Za a iya amince da rauni daga aboki, amma abokin gāba ko da ya sumbace ka kada ka sake da shi!
Adhonde moa kuom osiep inyalo geno, to jasigu medo mana nyoth mar masira.
7 Duk wanda ya ƙoshi da zuma, ba ya marmarinsa kuma amma wanda yake yunwa ko abin da yake da ɗaci ma zai ji shi da zaƙi.
Ngʼat moyiengʼ ok dwar mor kich, to ngʼatno modenyo kata mana gima kech mitne.
8 Kamar tsuntsun da ya ɓace daga sheƙarsa haka yake da mutumin da ya bar gidansa.
Mana kaka winyo mabayo moa e ode e kaka ngʼatno mabayo aa e dalane.
9 Man shafawa mai ƙanshi da kuma turare kan faranta zuciya, gaisuwar amini kuma takan fito daga shawarar kirki.
Moo mangʼwe ngʼar gi ubani kelo mor ne chuny, to ber mar osiep ngʼato wuok kuom ngʼado rieko gi adiera.
10 Kada ka manta da abokinka da kuma abokin mahaifinka, kuma kada ka tafi gidan ɗan’uwanka sa’ad da masifa ta same ka, gara ka je wurin maƙwabci na kusa da ka je wurin ɗan’uwan da yake da nisa.
Kik ijwangʼ osiepni kod osiep wuonu, to kik idhi e od owadu ka chandruok omaki, ber dhi ir jabuti machiegni moloyo owadu man mabor.
11 Ka zama mai hikima, ɗana, ka kuma faranta mini zuciya; zan iya amsa kowace irin suƙar da wani zai yi mini.
Bed mariek, wuoda kendo imi chunya mor eka anyalo dwoko ngʼato moro amora machaya.
12 Mai basira kan hango hatsari ya kuma kauce, marar azanci zai yi ta kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani.
Ngʼat mariek neno masira kabiro kendo opondo, to ngʼat mofuwo dhiyo adhiya nyime ma ohinyre.
13 A karɓe rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Kaw law ngʼatno mochungʼne ngʼat mokia kaka singo; kawe ka okete singo kar dhako mabayo.
14 In mutum ya albarkaci maƙwabcinsa da murya mai ƙarfi da sassafe, za a ɗauka shi a matsayin la’ana.
Ka ngʼato ogwedho jabute e lela gokinyi mangʼich, to ochalo mana gi ngʼama kwongʼe.
15 Mace mai fitina kamar ɗiɗɗigar ruwa take ba ƙaƙƙautawa;
Dhako ma jakoko chalo gi kodh ajiki,
16 hana ta yana kamar yin ƙoƙari tsai da iska ne ko yin ƙoƙarin cafke mai a tafin hannunka.
kwerogo chalo gi gengʼo yamo kata mako moo gi lwedo.
17 Kamar yadda ƙarfe kan wasa ƙarfe haka mutum kan koyi daga mutum.
Kaka nyinyo piago nyinyo, e kaka ngʼato piago nyawadgi.
18 Duk wanda ya lura da itacen ɓaure, zai ci’ya’yansa, kuma duk wanda ya lura da maigidansa za a girmama shi.
Ngʼat mopidho ngʼowu biro chamo olembe, to ngʼatno marito ruodhe ibiro miyo luor.
19 Kamar yadda ruwa kan nuna yadda fuska take, haka zuciyar mutum kan nuna irin mutumin.
Kirango pi, to wangʼi iwuon ema ineno, kendo kinono chunyi, to in iwuon ema inenori.
20 Mutuwa da Hallaka ba sa ƙoshi, haka idanun mutum ba sa ƙoshi da gani. (Sheol )
Tho kod kethruok ok rom ngangʼ, to kata mana wenge dhano bende ok rom. (Sheol )
21 Ana gwajin azurfa da kuma zinariya da wuta, amma akan gwada mutum ta wurin yabon da ya samu.
Dhahabu gi fedha itemo gi mach, to dhano itemo gi pak moyudo.
22 Ko da ka daka wawa a turmi, kana daka shi kamar hatsi da taɓarya, ba za ka fid da wauta daga gare shi ba.
Kata bed ni iyoko ngʼat mofuwo e pany, iyoke kaka cham miswago, ok inigol fupe oa kuome.
23 Ka tabbata ka san lafiyar garken tumakinka, ka mai da hankali ga garken shanunka;
Bed ni ingʼeyo maber kaka jambi chalo; bende rit maber kwethgi;
24 domin dukiya ba ta dawwama har abada, ba a kuma kasance da rawani daga tsara zuwa tsara.
nimar mwandu ok sik mochwere, to osimbo mar loch ok nobed ne tiengʼ ka tiengʼ.
25 Sa’ad da aka yanki ingirci sabon toho kuma ya bayyana aka kuma tattara ciyawa daga tuddai,
Ka ongʼad lum oko eka manyien twi, to ka ichoko ne jambi lum manie kor got,
26 gashin raguna za su tanada maka tufafi, za ka iya sayi gonaki masu kyau da kuɗin awaki.
eka iniyud yie rombe milosgo lewni, kendo iningʼiew lowo gi pesa miyudo kuom diek.
27 Za ka kasance da madarar awaki mai yawa don ka ciyar da kanka da kuma iyalinka ka kuma inganta bayinka mata.
Ibiro bedo gi chak mangʼeny mar diek ma ibiro pidhorigo gi joodi kendo pidho nyiri matiyoni.