< Karin Magana 25 >

1 Waɗannan ƙarin karin maganar Solomon ne waɗanda mutanen Hezekiya sarkin Yahuda suka tara.
Lezi ngezinye njalo izaga zikaSolomoni, ezabhalwa yizinceku zikaHezekhiya inkosi yakoJuda:
2 Ɗaukakar Allah ce a ɓoye batun; a bayyana batun kuwa ɗaukakar sarakuna ne.
Kuyinkazimulo kaNkulunkulu ukufihla indaba; ukuchwayisisa indaba ludumo lwababusi.
3 Kamar yadda sammai suna can bisa duniya kuma tana da zurfi, haka zukatan sarakuna suka wuce a bincika.
Njengalokhu izulu liphakeme lomhlaba ujulile, kanjalo imicabango yamakhosi kayifinyelelwa.
4 Ka tace azurfa sai kayan su fito don maƙerin azurfa;
Susa amakhafutha ahlangene lesiliva umkhandi athole ukulungisa isitsha sihle;
5 ka cire mugaye daga gaban sarki, kursiyinsa kuwa zai kahu ta wurin adalci.
susa abantu ababi phambi kwenkosi, isihlalo sayo sizaqiniswa ngokulunga.
6 Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki, kada kuma ka nemi wa kanka wuri a cikin manyan mutane;
Ungaziphakamisi phambi kwenkosi, ungaziphendleli indawo phakathi kwezikhulu;
7 gara ya ce maka, “Ka hauro nan,” da a ƙasƙantar da kai a gaban wani mai makami. Abin da ka gani da idanunka
kuba ngcono ukuthi yona ithi, “Woza uhlale ngapha,” kulokuthi yona ikwehlise phambi kwezikhulu. Lokho okubonileyo ngawakho amehlo
8 kada ka yi garaje kai ƙara a majalisa, gama me za ka yi a ƙarshe in maƙwabcinka ya ba ka kunya?
ungaphangisi ukukubika emthethwandaba, ngoba uzathini nxa umakhelwane wakho esekuyangisa?
9 In kai da maƙwabcinka kuka yi gardama, kada ka tona asirin wani,
Nxa ungaya edale lomakhelwane wakho ungahambi usuhlabela imfihlo yenu,
10 in ba haka ba duk wanda ya ji zai kunyata ka ba za ka kuma taɓa rabuwa da wannan mummuna suna ba.
funa lowo okuzwayo akuyangise uhlale usungumuntu olebizo elibi.
11 Kalmar da aka faɗa daidai tana kamar zubin zinariyar da aka yi a mazubin azurfa.
Ilizwi elikhulunywe ngesikhathi esifaneleyo linjengama-aphula egolide ananyekwe emcepheni wesiliva.
12 Kamar’yan kunnen zinariya ko kuwa kayan ado na zinariya zalla haka yake da tsawatawar mai hikima ga kunne mai saurarawa.
Njengecici legolide kumbe umceciso wegolide elicengiweyo kunjalo ukukhuza komuntu ohlakaniphileyo, kolalelayo.
13 Kamar sanyin ƙanƙara a lokacin girbi haka ɗan saƙo mai aminci wanda aka aika; ya wartsakar da ran waɗanda suka aike shi.
Njengokuqanda kongqwaqwane ngesikhathi sokuvuna sinjalo isithunywa esithembekileyo kwabasithumileyo; sivuselela imiphefumulo yabaphathi baso.
14 Kamar gizagizai da kuma iska marar ruwan sama haka mutumin da yake fariya a kan kyautan da ba ya bayarwa.
Njengamayezi lomoya okungalethi izulu unjalo umuntu ozikhukhumeza ngamandla angelawo.
15 Ta wurin haƙuri akan rinjaye mai mulki, magana mai hankali kan karye ƙashi.
Ngokubekezela inkosi ingancengwa ize ivume, lolimi oluthambileyo lungalephula ithambo.
16 In ka sami zuma, ka sha isashe kawai, in ya yi yawa, za ka yi amai.
Nxa uthole inyosi, dlana okwaneleyo ungedlulisi amalawulo, uzazihlanza.
17 Kada ka cika ziyarar gidan maƙwabcinka yawan ganinka zai sa ya ƙi ka.
Ungabi ngunsukuzonke endlini kamakhelwane wakho uzacina usumdaka abesekuzonda.
18 Kamar sanda ko takobi ko kibiya mai tsini haka yake da mutumin da yake ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinsa.
Unjengesagila loba inkemba kumbe umtshoko obukhali umuntu ofakaza amanga ngomakhelwane wakhe.
19 Kamar haƙori mai ciwo ko yin tafiya da gurguwar ƙafa haka yake ga mai dogara da marasa aminci a lokacin wahala.
Njengezinyo elibuhlungu loba unyawo olwenyeleyo kunjalo ukweyama emuntwini ongathembekanga ngesikhathi sokuhlupheka.
20 Kamar wanda ya tuɓe riga a ranar da ake sanyi, ko kuwa kamar zuba ruwan tsami a kanwa, haka yake da mai rera waƙoƙi ga mai baƙin ciki.
Njengomuntu okhumula ibhatshi mhla kumakhaza, loba njengokuthela iviniga phakathi kwesoda unjalo ohlabelela izingoma emuntwini odabukileyo.
21 In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ba shi abinci ya ci; in yana jin ƙishi, ka ba shi ruwa ya sha.
Nxa isitha sakho silambile siphe ukudla sidle; nxa somile siphe amanzi sinathe.
22 Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta mai ci a kansa, Ubangiji kuma zai sāka maka.
Ngokwenza lokho, umokhela amalahle avuthayo ekhanda, njalo uThixo uzakubusisa.
23 Kamar yadda iskar arewa kan kawo ruwan sama, haka jita-jita kan kawo fushi.
Njengomoya wasenyakatho uletha izulu, lunjalo ulimi olulobuqili luvusa ulaka.
24 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Kungcono ukuhlala ekhulusini lophahla lwendlu kulokuhlala ndlu yinye lomfazi olomlomo.
25 Kamar ruwan sanyi ga ran da ya gaji haka yake da jin labari mai daɗi daga ƙasa mai nisa.
Njengamanzi aqandayo emuntwini okhatheleyo, zinjalo izindaba ezimnandi ezivela elizweni elikude.
26 Kamar rafi mai laka ko rijiyar da ta gurɓace haka yake da mai adalci wanda ya miƙa wuya ga mugaye.
Njengesiziba esidungekileyo loba umthombo ongcolileyo unjalo umuntu olungileyo odedela umuntu omubi.
27 Ba shi da kyau ka sha zuma da yawa, haka ma ba shi da kyau ka nemi girma wa kanka.
Kakukuhle ukudla inyosi wedlulise, njalo kakulasithunzi ukuzidingela ukudunyiswa.
28 Kamar birni da katangarsa sun rushe haka yake da mutumin da ba ya iya danne fushinsa.
Njengedolobho eselidilikelwe ngumthangala walo unjalo umuntu ongazithintiyo.

< Karin Magana 25 >