< Karin Magana 25 >
1 Waɗannan ƙarin karin maganar Solomon ne waɗanda mutanen Hezekiya sarkin Yahuda suka tara.
Voici encore des paraboles de Salomon, qu’ont recueillies les hommes d’Ezéchias, roi de Juda.
2 Ɗaukakar Allah ce a ɓoye batun; a bayyana batun kuwa ɗaukakar sarakuna ne.
La gloire de Dieu est de cacher la parole, la gloire des rois, de scruter le discours.
3 Kamar yadda sammai suna can bisa duniya kuma tana da zurfi, haka zukatan sarakuna suka wuce a bincika.
Le ciel en haut et la terre en bas, et le cœur des rois est impénétrable.
4 Ka tace azurfa sai kayan su fito don maƙerin azurfa;
Ôte la rouille de l’argent, et il en sortira un vase très pur.
5 ka cire mugaye daga gaban sarki, kursiyinsa kuwa zai kahu ta wurin adalci.
Ôte l’impiété de devant le roi, et par la justice s’affermira son trône.
6 Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki, kada kuma ka nemi wa kanka wuri a cikin manyan mutane;
Ne parais pas chercher la gloire devant le roi, et ne te tiens pas parmi les grands.
7 gara ya ce maka, “Ka hauro nan,” da a ƙasƙantar da kai a gaban wani mai makami. Abin da ka gani da idanunka
Car il vaut mieux qu’on te dise: Monte ici, que d’être humilié devant le prince.
8 kada ka yi garaje kai ƙara a majalisa, gama me za ka yi a ƙarshe in maƙwabcinka ya ba ka kunya?
Ce que tes yeux ont vu, ne le publie pas aussitôt dans une querelle; de peur que dans la suite, tu ne puisses réparer ton tort, lorsque tu auras déshonoré ton ami.
9 In kai da maƙwabcinka kuka yi gardama, kada ka tona asirin wani,
Traite ton affaire avec ton ami, et ne révèle pas un secret à un étranger;
10 in ba haka ba duk wanda ya ji zai kunyata ka ba za ka kuma taɓa rabuwa da wannan mummuna suna ba.
De peur qu’il ne t’insulte, lorsqu’il t’aura appris, et qu’il ne cesse de te le reprocher. La faveur et l’amitié délivrent; conserve-les, afin que tu ne deviennes pas répréhensible.
11 Kalmar da aka faɗa daidai tana kamar zubin zinariyar da aka yi a mazubin azurfa.
Comme sont les pommes d’or, sur des lits d’argent, ainsi est celui qui dit une parole en son temps.
12 Kamar’yan kunnen zinariya ko kuwa kayan ado na zinariya zalla haka yake da tsawatawar mai hikima ga kunne mai saurarawa.
C’est un pendant d’oreille d’or, et une perle brillante que celui qui reprend un sage et une oreille obéissante.
13 Kamar sanyin ƙanƙara a lokacin girbi haka ɗan saƙo mai aminci wanda aka aika; ya wartsakar da ran waɗanda suka aike shi.
Comme la fraîcheur de la neige, au jour de la moisson, ainsi est un messager fidèle pour celui qui l’a envoyé; il fait reposer son âme.
14 Kamar gizagizai da kuma iska marar ruwan sama haka mutumin da yake fariya a kan kyautan da ba ya bayarwa.
Des nuages, du vent et point de pluie à la suite, tel est l’homme qui se vante et ne remplit pas ses promesses.
15 Ta wurin haƙuri akan rinjaye mai mulki, magana mai hankali kan karye ƙashi.
Par la patience, un prince se laissera fléchir, et une langue douce brisera la dureté.
16 In ka sami zuma, ka sha isashe kawai, in ya yi yawa, za ka yi amai.
Tu as trouvé du miel: mange ce qui te suffit de peur que, rassasié, tu ne le vomisses.
17 Kada ka cika ziyarar gidan maƙwabcinka yawan ganinka zai sa ya ƙi ka.
Éloigne ton pied de la maison de ton prochain; de peur qu’un jour, rassasié de toi, il ne te haïsse.
18 Kamar sanda ko takobi ko kibiya mai tsini haka yake da mutumin da yake ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinsa.
Un trait, un glaive, une flèche acérée, tel est l’homme qui, contre son prochain, dit un faux témoignage.
19 Kamar haƙori mai ciwo ko yin tafiya da gurguwar ƙafa haka yake ga mai dogara da marasa aminci a lokacin wahala.
Une dent cariée, un pied lassé, tel est celui qui espère en un infidèle au jour de l’angoisse,
20 Kamar wanda ya tuɓe riga a ranar da ake sanyi, ko kuwa kamar zuba ruwan tsami a kanwa, haka yake da mai rera waƙoƙi ga mai baƙin ciki.
Et qui perd son manteau au jour du froid. Il met du vinaigre dans du nitre, celui qui chante des cantiques à un cœur très mauvais. Comme la teigne au vêtement et le ver au bois, ainsi la tristesse de l’homme nuit à son cœur.
21 In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ba shi abinci ya ci; in yana jin ƙishi, ka ba shi ruwa ya sha.
Si ton ennemi a faim, donne-lui à manger: s’il a soif, donne-lui de l’eau à boire;
22 Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta mai ci a kansa, Ubangiji kuma zai sāka maka.
Car tu amasseras des charbons ardents sur sa tête; et le Seigneur te le rendra.
23 Kamar yadda iskar arewa kan kawo ruwan sama, haka jita-jita kan kawo fushi.
Le vent d’aquilon dissipe les pluies, et le visage triste, la langue médisante.
24 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Mieux vaut demeurer sur l’angle d’un toit qu’avec une femme querelleuse, et dans une maison commune.
25 Kamar ruwan sanyi ga ran da ya gaji haka yake da jin labari mai daɗi daga ƙasa mai nisa.
C’est de l’eau fraîche à une âme altérée, qu’une bonne nouvelle venant d’une terre éloignée.
26 Kamar rafi mai laka ko rijiyar da ta gurɓace haka yake da mai adalci wanda ya miƙa wuya ga mugaye.
Une fontaine troublée avec le pied, et une source corrompue, tel est le juste qui tombe devant l’impie.
27 Ba shi da kyau ka sha zuma da yawa, haka ma ba shi da kyau ka nemi girma wa kanka.
Comme manger beaucoup de miel n’est pas une bonne chose; ainsi celui qui scrute la majesté sera accablé par la gloire.
28 Kamar birni da katangarsa sun rushe haka yake da mutumin da ba ya iya danne fushinsa.
Comme est une ville ouverte, et sans enceinte de murailles; ainsi est l’homme qui ne peut, en parlant, retenir son esprit.