< Karin Magana 24 >
1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
No tengas envidia de los malvados, ni desees su compañía,
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
porque ellos conspiran planes crueles y discuten entre ellos para causar tribulación.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Una casa se construye con sabiduría. Su fundamento seguro es la inteligencia.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
Sus habitaciones están llenas de conocimiento, con todo tipo de hermosos y valiosos objetos.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
Si tienes sabiduría, serás fuerte. Si tienes inteligencia, tu poder aumentará.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Porque con la guía correcta, podrás ir a la guerra, y serás victorioso si tienes muchos buenos consejeros.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
La sabiduría examina las mentes de los tontos. Ellos no tienen nada que aportar en las discusiones sobre los asuntos importantes.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Todo aquel que hace planes para hacer el mal, será considerado un problemático.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Los planes que hacen los tontos son de pecado. Todos aborrecen a los que se burlan de otros.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Si te rindes en el momento de la prueba, mostraras cuan débil eres.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Rescata a los que son expulsados para ser ejecutados. Salva a los que desfallecen de camino a su muerte.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Si dices: “No sabíamos nada sobre esto”, ¿no crees que el Dios que juzga las motivaciones no se dará cuenta de lo que ocurre realmente? El que te mira desde arriba lo sabe todo, y le pagará a todos según sus actos.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Hijo mío, comer miel te conviene; el panal de miel tiene un dulce sabor.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Del mismo modo, debes saber que te conviene la sabiduría; y que sin la encuentras habrá un futuro para ti que no será frustrado.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
No seas como el criminal que espera para entrar por sorpresa en las casas de las buenas personas. No ataques el lugar donde viven.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Los que hacen el bien podrán caer siete veces, y aun así se levantaran; pero el desastre vendrá para derribar a los malvados.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
No celebres cuando tu enemigo caiga. No te alegues cuando se tropiece,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
porque puede que cuando el Señor lo note, se desagrade de ti y no lo castigue como lo había pensado.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
No te enojes por causa de los malvados, ni sientas celos por los que hacen el mal,
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
porque los malvados no tienen futuro. La lámpara de los malvados se apagará.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Hijo mío, honra al Señor y al rey, y no te juntes con los rebeldes,
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
porque el desastre vendrá sobre ellos repentinamente. ¿Quién podrá saber cómo los castigarán el Señor y el rey?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Estos son más dichos del sabio: Mostrar preferencias cuando emites un juicio no es bueno.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Los que le dicen al culpable: “Eres inocente”, serán malditos por el pueblo y odiados por la nación,
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
pero los que condenan al culpable serán estimados, y recibirán rica bendición.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Una respuesta honesta es como un beso en los labios.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Haz primero el trabajo que necesitas hacer afuera y prepárate para sembrar tus campos. Solo después de eso, comienza a construir tu casa.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
No seas testigo contra tu prójimo sin tener una buena razón, ni digas mentiras.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
No digas en tu pensamiento: “Voy a hacerle lo mismo que me hizo! ¡Haré que me pague por lo que ha hecho!”
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Mientras caminaba, pasé por el campo del hombre perezoso, y por el viñedo de un insensato.
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
Y estaba lleno de monte y espinas, el suelo estaba cubierto de hierba y la piedra angular se había caído.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Y mientras veía, pensé y aprendí una lección:
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Puedes decir: “Solo dormiré un poco más, me recostaré apenas un rato, y cruzaré mis brazos para descansar un poco más”,
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
pero la pobreza te atacará como un ladrón, y la miseria como un guerrero armado.