< Karin Magana 24 >
1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
ne aemuleris viros malos nec desideres esse cum eis
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
quia rapinas meditatur mens eorum et fraudes labia eorum loquuntur
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
sapientia aedificabitur domus et prudentia roborabitur
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
in doctrina replebuntur cellaria universa substantia pretiosa et pulcherrima
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
vir sapiens et fortis est et vir doctus robustus et validus
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
quia cum dispositione initur bellum et erit salus ubi multa consilia sunt
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
excelsa stulto sapientia in porta non aperiet os suum
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
qui cogitat malefacere stultus vocabitur
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
cogitatio stulti peccatum est et abominatio hominum detractor
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
si desperaveris lassus in die angustiae inminuetur fortitudo tua
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
erue eos qui ducuntur ad mortem et qui trahuntur ad interitum liberare ne cesses
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
si dixeris vires non suppetunt qui inspector est cordis ipse intellegit et servatorem animae tuae nihil fallit reddetque homini iuxta opera sua
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
comede fili mi mel quia bonum est et favum dulcissimum gutturi tuo
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
sic et doctrina sapientiae animae tuae quam cum inveneris habebis in novissimis et spes tua non peribit
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
ne insidieris et quaeras impietatem in domo iusti neque vastes requiem eius
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
septies enim cadet iustus et resurget impii autem corruent in malum
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
cum ceciderit inimicus tuus ne gaudeas et in ruina eius ne exultet cor tuum
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
ne forte videat Dominus et displiceat ei et auferat ab eo iram suam
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
ne contendas cum pessimis nec aemuleris impios
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
quoniam non habent futurorum spem mali et lucerna impiorum extinguetur
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
time Dominum fili mi et regem et cum detractoribus non commiscearis
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
quoniam repente consurget perditio eorum et ruinam utriusque quis novit
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
haec quoque sapientibus cognoscere personam in iudicio non est bonum
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
qui dicit impio iustus es maledicent ei populi et detestabuntur eum tribus
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
qui arguunt laudabuntur et super ipsos veniet benedictio
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
labia deosculabitur qui recta verba respondet
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
praepara foris opus tuum et diligenter exerce agrum tuum ut postea aedifices domum tuam
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
ne sis testis frustra contra proximum tuum nec lactes quemquam labiis tuis
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
ne dicas quomodo fecit mihi sic faciam ei reddam unicuique secundum opus suum
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
per agrum hominis pigri transivi et per vineam viri stulti
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
et ecce totum repleverant urticae operuerant superficiem eius spinae et maceria lapidum destructa erat
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
quod cum vidissem posui in corde meo et exemplo didici disciplinam
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
parum inquam dormies modicum dormitabis pauxillum manus conseres ut quiescas
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
et veniet quasi cursor egestas tua et mendicitas quasi vir armatus