< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Non invidiare gli uomini malvagi, non desiderare di stare con loro;
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
poiché il loro cuore trama rovine e le loro labbra non esprimono che malanni.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Con la sapienza si costruisce la casa e con la prudenza la si rende salda;
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
con la scienza si riempiono le sue stanze di tutti i beni preziosi e deliziosi.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
Un uomo saggio vale più di uno forte, un uomo sapiente più di uno pieno di vigore,
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
perché con le decisioni prudenti si fa la guerra e la vittoria sta nel numero dei consiglieri.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
E' troppo alta la sapienza per lo stolto, alla porta della città egli non potrà aprir bocca.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Chi trama per fare il male si chiama mestatore.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Il proposito dello stolto è il peccato e lo spavaldo è l'abominio degli uomini.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Se ti avvilisci nel giorno della sventura, ben poca è la tua forza.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Libera quelli che sono condotti alla morte e salva quelli che sono trascinati al supplizio.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Se dici: «Ecco, io non ne so nulla», forse colui che pesa i cuori non lo comprende? Colui che veglia sulla tua vita lo sa; egli renderà a ciascuno secondo le sue opere.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Mangia, figlio mio, il miele, perché è buono e dolce sarà il favo al tuo palato.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Sappi che tale è la sapienza per te: se l'acquisti, avrai un avvenire e la tua speranza non sarà stroncata.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Non insidiare, o malvagio, la dimora del giusto, non distruggere la sua abitazione,
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
perché se il giusto cade sette volte, egli si rialza, ma gli empi soccombono nella sventura.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Non ti rallegrare per la caduta del tuo nemico e non gioisca il tuo cuore, quando egli soccombe,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
perché il Signore non veda e se ne dispiaccia e allontani da lui la collera.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Non irritarti per i malvagi e non invidiare gli empi,
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
perché non ci sarà avvenire per il malvagio e la lucerna degli empi si estinguerà.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Temi il Signore, figlio mio, e il re; non ribellarti né all'uno né all'altro,
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
perché improvvisa sorgerà la loro vendetta e chi sa quale scempio faranno l'uno e l'altro?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Anche queste sono parole dei saggi. Aver preferenze personali in giudizio non è bene.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Se uno dice all'empio: «Tu sei innocente», i popoli lo malediranno, le genti lo esecreranno,
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
mentre tutto andrà bene a coloro che rendono giustizia, su di loro si riverserà la benedizione.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Dà un bacio sulle labbra colui che risponde con parole rette.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Sistema i tuoi affari di fuori e fatti i lavori dei campi e poi costruisciti la casa.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Non testimoniare alla leggera contro il tuo prossimo e non ingannare con le labbra.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Non dire: «Come ha fatto a me così io farò a lui, renderò a ciascuno come si merita».
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Sono passato vicino al campo di un pigro, alla vigna di un uomo insensato:
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
ecco, ovunque erano cresciute le erbacce, il terreno era coperto di cardi e il recinto di pietre era in rovina.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Osservando, riflettevo e, vedendo, ho tratto questa lezione:
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
un pò dormire, un pò sonnecchiare, un pò incrociare le braccia per riposare
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
e intanto viene passeggiando la miseria e l'indigenza come un accattone.

< Karin Magana 24 >