< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
MAI kuko oe i ka aoao o na kanaka hewa, Aole makemake hoi e noho pu me lakou.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
No ka mea, noonoo ae la ko lakou naau i ka mea e make ai, A no ka ino hoi ko lakou lehelehe e kamailio ai.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Ma ke akamai i kukuluia'i ka hale, Ma ka naauao hoi ia i hookupaaia'i.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
Na ka ike e hoopihaia'i na keena, I na waiwai a pau, he maikai no a he nani hoi.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
O ke kanaka naauao, he ikaika no ia; E mahuahua ana no ka ikaika o ke kanaka ike.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
No ka mea, ma ka noonoo nui oe e kaua aku ai, A he ola no ma ka nui o ka poe kukakuka pu.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
He kiekie loa ka naauao maluna o ka mea naaupo; Aole e oaka kona waha ma ka ipuka.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
O ka mea noonoo e hana hewa aku, E kapaia'ku ia he mea hana kolohe.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
O ka manao lapuwale, he hewa ia; A he hoopailua i na kanaka ka mea hoowahawaha.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Ina pauaho oe i kou la popilikia, Uuku wale no kou ikaika.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Ina e hookaulua oe e hoopakele i ka poe i hana paa ia e make, A me ka poe e kokoke ana i ka pepehiia mai;
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Ina e i ae oe, E, aole makou i ike; Aole anei e noonoo mai ka mea nana e kaupaona na naau? A o ka mea hoi nana e malama i ka uhane, aole anei oia e ike? Aole anei oia e hoopai i ke kanaka e like me kana hana ana?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
E kuu keiki, e ai iho oe i ka meli, no ka mea, he maikai ia; A i ka waihona meli hoi he ono ia i kou waha;
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Pela hoi ka ike ana i ka naauao i kou uhane; A i loaa ia oe, alaila he hope, A o kou manaolana aole ia e poho.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Mai hoohalua, e ke kanaka hewa, ma ka hale o ka mea pono; Mai powa aku oe ma kona wahi e moe ai.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
No ka mea, ehiku no ka haule ana o ka mea pono, a ala hou mai no; O ka poe hewa, e hina no lakou iloko o ka poino.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
I ka haule ana o kou euemi, mai hauoli oe, I koua hina ana hoi mai olioli kou naau;
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
O ike mai Iehova he hewa ia i kona mau maka, A e hoohuli oia i kona huhu mai ona aku.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Mai ukiuki oe no ka poe hewa, Aole hoi e kuko i ka noho ana o ka poe hana ino.
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
No ka mea, aohe uku maikai no ka mea hewa; O ke kukui o ka poe hewa, e pio ana no ia.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
E kuu keiki, e makau aku ia Iehova, a me ke alii; Me ka poe lolelua ka naau, mai launa aku.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
No ka mea, e hiki wawe mai ko lakou poino; A o ka make ana o laua a elua, owai ka mea ike aku?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Na ka poe naauao hoi keia mau mea: O ka manao kapakahi ma ka hookolokolo ana, aole i pono ia.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
O ka mea olelo aku i ka mea hewa, He pono no oe; E hoino aku no na kanaka ia ia, E hoowahawaha hoi na lahuikanaka ia ia.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Aka, he oluolu ko ka poe i ao aku, E hiki mai hoi ia lakou ka pomaikai io.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
E honiia'ku na lehelehe O ka mea olelo aku ma ka pololei.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Muwaho e hoomakaukau ai i kau hana, A e hooponopono nou iho ma ke kula; A mahope iho, e kukula ae i kou hale.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Mai liio hala ole oe i hoike ku e i kou hoanoho; Aole hoi e hoopunipuni me kou mau lehelehe.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Mai olelo oe, E like me ia i hana mai ai ia'u, pela au e hana aku ai ia ia; E hoopai aku au i ke kanaka e like me kana hana ana.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Ma ke kihapai o ka mea palaualelo i maalo ai au, Ma ka pawaina hoi o ke Kanaka noonoo ole:
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
Aia hoi, ulu paapu ae la ka puakala, Uhi mai la maluna ona na kakalaioa, O kona pa pohaku hoi, ua hiolo iho la ia.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Nana aku la au, halalo iho la ko'u naau; Ike iho la au, a loaa ia'u ke aoia mai.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
He moe iki ae, he hiamoe iki ae, He pelu hou iki ae i na lima a hiamoe;
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
A e hiki mai kou ilihune me he kanaka hele la, A me kou nele e like me ke kanaka kaua.

< Karin Magana 24 >