< Karin Magana 24 >
1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Folge nicht bösen Leuten und wünsche nicht, bei ihnen zu sein.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
Denn ihr Herz trachtet nach Schaden, und ihre Lippen raten zu Unglück.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Durch Weisheit wird ein Haus gebauet und durch Verstand erhalten.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
Durch ordentlich Haushalten werden die Kammern voll aller köstlichen, lieblichen Reichtümer.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
Ein weiser Mann ist stark und ein vernünftiger Mann ist mächtig von Kräften.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Denn mit Rat muß man Krieg führen; und wo viel Ratgeber sind, da ist der Sieg.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Weisheit ist dem Narren zu hoch; er darf seinen Mund im Tor nicht auftun.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Wer ihm selbst Schaden tut, den heißt man billig einen Erzbösewicht.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Des Narren Tücke ist Sünde; und der Spötter ist ein Greuel vor den Leuten.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Der ist nicht stark, der in der Not nicht fest ist.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Errette die, so man töten will, und entzieh dich nicht von denen, die man würgen will.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Sprichst du: Siehe, wir verstehen's nicht; meinest du nicht, der die Herzen weiß, merket es, und der auf die Seele acht hat, kennet es und vergilt dem Menschen nach seinem Werk?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Iß, mein Sohn, Honig, denn es ist gut, und Honigseim ist süß in deinem Halse.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Also lerne die Weisheit für deine Seele. Wenn du sie findest, so wird's hernach wohlgehen, und deine Hoffnung wird nicht umsonst sein.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Laure nicht, als ein Gottloser, auf das Haus des Gerechten; verstöre seine Ruhe nicht!
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Denn ein Gerechter fällt siebenmal und stehet wieder auf; aber die Gottlosen versinken in Unglück.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Freue dich des Falles deines Feindes nicht, und dein Herz sei nicht froh über seinem Unglück;
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
es möchte der HERR sehen und ihm übel gefallen und seinen Zorn von ihm wenden.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Erzürne dich nicht über den Bösen und eifre nicht über die Gottlosen;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
denn der Böse hat nichts zu hoffen, und die Leuchte der Gottlosen wird verlöschen.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Mein Kind, fürchte den HERRN und den König und menge dich nicht unter die Aufrührerischen!
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
Denn ihr Unfall wird plötzlich entstehen; und wer weiß, wann beider Unglück kommt?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Dies kommt auch von den Weisen: Die Person ansehen im Gericht ist nicht gut.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Wer zum Gottlosen spricht: Du bist fromm, dem fluchen die Leute und hasset das Volk.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Welche aber strafen, die gefallen wohl, und kommt ein reicher Segen auf sie.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Eine richtige Antwort ist wie ein lieblicher Kuß.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Richte draußen dein Geschäft aus und arbeite deinen Acker; danach baue dein Haus.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Sei nicht Zeuge ohne Ursache wider deinen Nächsten und betrüge nicht mit deinem Munde!
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Sprich nicht: Wie man mir tut, so will ich wieder tun und einem jeglichen sein Werk vergelten.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Ich ging vor dem Acker des Faulen und vor dem Weinberge des Narren,
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
und siehe, da waren eitel Nesseln drauf und stund voll Disteln, und die Mauer war eingefallen.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Da ich das sah, nahm ich's zu Herzen und schauete und lernete dran.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Du willst ein wenig schlafen und ein wenig schlummern und ein wenig die Hände zusammentun, daß du ruhest;
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
aber es wird dir deine Armut kommen wie ein Wanderer und dein Mangel wie ein gewappneter Mann.