< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Ne porte point envie aux hommes méchants, et ne désire point être avec eux.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
Car leur cœur médite la ruine et leurs lèvres parlent de nuire.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
C'est par la sagesse que la maison sera bâtie, et c'est par l'intelligence qu'elle sera affermie.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
Et c'est par la science que les chambres seront remplies de tous les biens précieux et agréables.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
L'homme sage est plein de force, et l'homme intelligent devient puissant.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Car c'est avec la prudence qu'on fait la guerre, et la victoire dépend du nombre des conseillers.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
La sagesse est trop élevée pour un insensé; il n'ouvrira pas la bouche aux portes.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Celui qui pense à faire mal, on l'appellera maître en méchanceté.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Un mauvais dessein est une folie, et le moqueur est en abomination aux hommes.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Si tu perds courage au jour de la détresse, ta force sera petite.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Délivre ceux qui sont traînés à la mort, et qui sont sur le point d'être tués.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Si tu dis: Voici, nous n'en avons rien su; celui qui pèse les cœurs ne l'entendra-t-il point? Et celui qui garde ton âme ne le saura-t-il point? Et ne rendra-t-il pas à chacun selon son œuvre?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Mon fils, mange le miel, car il est bon, et le rayon de miel, qui est doux à ton palais.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Telle sera la connaissance de la sagesse à ton âme; quand tu l'auras trouvée, il y aura une bonne issue, et ton attente ne sera point trompée.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Méchant, ne tends pas d'embûches contre la demeure du juste, et ne dévaste pas son habitation.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Car le juste tombera sept fois, et il sera relevé; mais les méchants sont précipités dans le malheur.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Quand ton ennemi sera tombé, ne t'en réjouis point; et quand il sera renversé, que ton cœur ne s'en égaie point;
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
De peur que l'Éternel ne le voie, et que cela ne lui déplaise, et qu'il ne détourne de lui sa colère.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Ne t'irrite point à cause de ceux qui font le mal; ne porte point envie aux méchants;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
Car il n'y a pas d'issue pour celui qui fait le mal, et la lampe des méchants sera éteinte.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Mon fils, crains l'Éternel et le roi, et ne te mêle point avec des gens remuants.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
Car leur ruine surviendra tout d'un coup, et qui sait le malheur qui arrivera aux uns et aux autres?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Voici encore ce qui vient des sages: Il n'est pas bon d'avoir égard à l'apparence des personnes dans le jugement.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Celui qui dit au méchant: Tu es juste, les peuples le maudiront, et les nations le détesteront.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Mais ceux qui le reprennent s'en trouveront bien; sur eux viendront la bénédiction et le bonheur.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Celui qui répond avec droiture à quelqu'un, lui donne un baiser sur les lèvres.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Règle ton ouvrage au-dehors, et mets ordre à ton champ; et puis tu bâtiras ta maison.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Ne sois point témoin contre ton prochain sans qu'il soit nécessaire: voudrais-tu séduire par tes lèvres?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Ne dis point: Je lui ferai comme il m'a fait; je rendrai à cet homme selon son œuvre.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
J'ai passé près du champ d'un paresseux, et près de la vigne d'un homme dépourvu de sens;
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
Et voici, les chardons y croissaient partout; les ronces en couvraient la surface, et son mur de pierre était écroulé.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Quand je vis cela, j'y appliquai mes pensées; je le regardai, j'en tirai instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un peu dormir, un peu sommeiller, un peu croiser les mains pour se reposer,
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
Et ta pauvreté viendra comme un passant, et ta disette comme un homme armé.

< Karin Magana 24 >