< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Ne porte point d'envie aux hommes malins, et ne désire point d'être avec eux.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
Car leur cœur pense à piller, et leurs lèvres parlent de nuire.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
La maison sera bâtie par la sagesse, et sera affermie par l'intelligence.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
Et par la science les cabinets seront remplis de tous les biens précieux et agréables.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
L'homme sage [est accompagné] de force, et l'homme qui a de l'intelligence renforce la puissance.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Car par la prudence tu feras la guerre avantageusement, et la délivrance consiste dans le nombre des conseillers.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Il n'y a point de sagesse qui ne soit trop haute pour le fou; il n'ouvrira point sa bouche à la porte.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Celui qui pense à faire mal, on l'appellera, Songe-malice.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Le discours de la folie n'est que péché, et le moqueur est en abomination à l'homme.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Si tu as perdu courage dans la calamité, ta force s'est diminuée.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Si tu te retiens pour ne délivrer point ceux qui sont traînés à la mort, et qui sont sur le point d'être tués,
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Parce que tu diras: Voici, nous n'en avons rien su; celui qui pèse les cœurs ne l'entendra-t-il point? et celui qui garde ton âme, ne le saura-t-il point? et ne rendra-t-il point à chacun selon son œuvre?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Mon fils, mange le miel, car il est bon; et le rayon de miel, car il est doux à ton palais.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Ainsi sera à ton âme la connaissance de la sagesse, quand tu l'auras trouvée; et il y aura une [bonne] issue, et ton attente ne sera point retranchée.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Méchant, n'épie point le domicile du juste, et ne détruis point son gîte.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Car le juste tombera sept fois, et sera relevé; mais les méchants tombent dans le mal.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Quand ton ennemi sera tombé, ne t'en réjouis point; et quand il sera renversé, que ton cœur ne s'en égaye point;
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
De peur que l'Eternel ne [le] voie, et que cela ne lui déplaise, tellement qu'il détourne de dessus lui sa colère [sur toi.]
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Ne te dépite point à cause des gens malins; ne porte point d'envie aux méchants;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
Car il n'y aura point de [bonne] issue pour le méchant, et la lampe des méchants sera éteinte.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Mon fils, crains l'Eternel, et le Roi; et ne te mêle point avec des gens remuants.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
Car leur calamité s'élèvera tout d'un coup; et qui sait l'inconvénient qui arrivera à ces deux-là?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Ces choses aussi sont pour les sages. Il n'est pas bon d'avoir égard à l'apparence des personnes en jugement.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Celui qui dit au méchant: Tu es juste, les peuples le maudiront, et les nations l'auront en détestation.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Mais pour ceux qui le reprennent, ils en retireront de la satisfaction, et la bénédiction que les biens accompagnent se répandra sur eux.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Celui qui répond avec justesse fait plaisir [à celui qui l'écoute.]
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Range ton ouvrage dehors, et l'apprête au champ qui est à toi, et puis bâtis ta maison.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Ne sois point témoin contre ton prochain, sans qu'il en soit besoin; car voudrais-tu t'en faire croire par tes lèvres?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Ne dis point: comme il m'a fait, ainsi lui ferai-je; je rendrai à cet homme selon ce qu'il m'a fait.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
J'ai passé près du champ de l'homme paresseux, et près de la vigne de l'homme dépourvu de sens;
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
Et voilà, tout y était monté en chardons, et les orties avaient couvert le dessus, et sa cloison de pierres était démolie.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Et ayant vu cela, je le mis dans mon cœur, je le regardai, j'en reçus de l'instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un peu de dormir, un peu de sommeil, un peu de ploiement de bras pour demeurer couché,
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
Et ta pauvreté viendra [comme] un passant; et ta disette, comme un soldat.

< Karin Magana 24 >