< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
N’envie pas les hommes qui font le mal, et ne désire pas d’être avec eux,
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
car leur cœur médite la destruction, et leurs lèvres parlent de tourment.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Par la sagesse la maison est bâtie, et elle est établie par l’intelligence;
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
et par la connaissance les chambres sont remplies de tous les biens précieux et agréables.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
L’homme sage a de la force, et l’homme de connaissance affermit sa puissance;
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
car sous une [sage] direction tu feras ta guerre, et le salut est dans le grand nombre des conseillers.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
La sagesse est trop haute pour le fou, il n’ouvrira pas la bouche dans la porte.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Celui qui pense à mal faire, on l’appellera intrigant.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Le plan de la folie est péché, et le moqueur est en abomination aux hommes.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Si tu perds courage au jour de la détresse, ta force est mince.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Délivre ceux qui sont menés à la mort, et ne te retire pas de ceux qui chancellent vers une mort violente.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Si tu dis: Voici, nous n’en savions rien; celui qui pèse les cœurs, lui ne le considérera-t-il pas? et celui qui garde ton âme, lui le sait; et il rend à l’homme selon son œuvre.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Mon fils, mange du miel, car il est bon; et un rayon de miel est doux à ton palais.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Ainsi connais pour ton âme la sagesse: si tu l’as trouvée, il y a un avenir, et ton attente ne sera point réduite à néant.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Méchant, ne mets pas des embûches contre l’habitation du juste, ne dévaste pas son gîte.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Car le juste tombe sept fois, et se relève; mais les méchants trébuchent [pour tomber] dans le malheur.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Si ton ennemi tombe, ne te réjouis pas; et s’il trébuche, que ton cœur ne s’égaie pas;
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
de peur que l’Éternel ne le voie, et que cela ne soit mauvais à ses yeux, et qu’il ne détourne de dessus lui sa colère.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Ne t’irrite pas à cause de ceux qui font le mal, n’envie pas les méchants;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
car il n’y a pas d’avenir pour l’inique: la lampe des méchants s’éteindra.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Mon fils, crains l’Éternel et le roi; ne te mêle pas avec les gens remuants,
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
car leur calamité surgira tout à coup; et qui sait la ruine des uns et des autres?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Ces choses aussi viennent des sages: Faire acception des personnes dans le jugement n’est pas bien.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Celui qui dit au méchant: Tu es juste, les peuples le maudiront, les peuplades seront indignées contre lui;
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
mais ceux qui le reprennent seront agréables, et une bénédiction de bien viendra sur eux.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Celui qui répond des paroles justes embrasse les lèvres.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prépare ton ouvrage au-dehors, et mets en état ton champ, et après, bâtis ta maison.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Ne sois pas témoin, sans motif, contre ton prochain; voudrais-tu donc tromper de tes lèvres?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Ne dis pas: Comme il m’a fait, je lui ferai; je rendrai à l’homme selon son œuvre.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
J’ai passé près du champ de l’homme paresseux et près de la vigne de l’homme dépourvu de sens,
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
et voici, tout y était monté en chardons; les orties en avaient couvert la surface, et sa clôture de pierres était démolie.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Et je regardai, j’y appliquai mon cœur; je vis, [et] je reçus instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Un peu de sommeil, un peu d’assoupissement, un peu croiser les mains pour dormir…,
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
et ta pauvreté viendra [comme] un voyageur, et ton dénuement comme un homme armé.

< Karin Magana 24 >