< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Do not be envious of evil men, And do not desire to be with them.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
For their heart meditates [on] destruction, And their lips speak perverseness.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
A house is built by wisdom, And it establishes itself by understanding.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
And the inner parts are filled by knowledge, [With] all precious and pleasant wealth.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
The wise [is] mighty in strength, And a man of knowledge is strengthening power,
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
For you make war for yourself by plans, And deliverance [is] in a multitude of counselors.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdom [is] high for a fool, he does not open his mouth in the gate.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Whoever is devising to do evil, They call him a master of wicked thoughts.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The thought of folly [is] sin, And a scorner [is] an abomination to man.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
You have showed yourself weak in a day of adversity, Your power is restricted,
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
If [from] delivering those taken to death, And you take back those slipping to the slaughter.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
When you say, “Behold, we did not know this.” Is the Ponderer of hearts not He who understands? And the Keeper of your soul He who knows? And He has rendered to man according to his work.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
My son, eat honey that [is] good, And the honeycomb [is] sweet to your palate.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
So [is] the knowledge of wisdom to your soul, If you have found that there is a posterity And your hope is not cut off.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Do not lay wait, O wicked one, At the habitation of the righteous. Do not spoil his resting place.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For the righteous fall and rise seven [times], And the wicked stumble in evil.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Do not rejoice in the falling of your enemy, And do not let your heart be joyful in his stumbling,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Lest YHWH see, and [it be] evil in His eyes, And He has turned His anger from off him.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Do not fret yourself at evildoers, do not be envious at the wicked,
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For there is not a posterity to the evil, The lamp of the wicked is extinguished.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Fear YHWH, my son, and the king, Do not mix yourself up with changers,
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
For their calamity rises suddenly, And the ruin of them both—who knows!
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
These are also for the wise: [It] is not good to discern faces in judgment.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Whoever is saying to the wicked, “You [are] righteous,” Peoples execrate him—nations abhor him.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
And it is pleasant to those reproving, And a good blessing comes on them.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
He who is returning straightforward words kisses lips.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare your work in an out-place, And make it ready in the field—go afterward, Then you have built your house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Do not be a witness against your neighbor for nothing, Or you have enticed with your lips.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Do not say, “As he did to me, so I do to him, I render to each according to his work.”
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
I passed by near the field of a slothful man, And near the vineyard of a man lacking heart.
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
And behold, it has gone up—all of it—thorns! Nettles have covered its face, And its stone wall has been broken down.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
And I see—I set my heart, I have seen—I have received instruction,
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
A little sleep—a little slumber—A little folding of the hands to lie down.
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
And your poverty has come [as] a traveler, And your want as an armed man!

< Karin Magana 24 >