< Karin Magana 24 >
1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Be thou not envious of bad men, and do not long to be with them.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
For their heart meditateth destruction, and of mischief do their lips speak.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Through wisdom is a house built; and through understanding is it firmly established;
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
And through knowledge are chambers filled with all manner of precious and pleasant wealth.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
A wise man is [always] in power; and a man of knowledge fortifieth [his] strength.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
For by wise counsel canst thou conduct thy war; and there is help in a multitude of counsellors.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdom is too high for a fool: in the gate can he not open his mouth.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Him that deviseth to do evil, men call a master of wicked devices.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The counsel of folly is sin; and an abomination to men is the scorner.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
If thou despond on the day of distress, thy strength is small.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Deliver those that are taken unto death, and those that are moved away to the slaughter hold back.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
If thou shouldst say, Behold, we know not this man: lo, he that weigheth hearts will truly regard it, and he that keepeth thy soul will surely know it; and he will give a recompense to man according to his doing.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Eat honey, my son, because it is good; and the fine honey, which is sweet to thy palate:
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
So obtain the knowledge of wisdom for thy soul: when thou hast found her, then shall there be a [happy] future, and thy hope shall not be cut off.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Lie not in wait, O wicked man! against the dwelling of the righteous; waste not his resting-place;
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For though the righteous were to fall seven times, he will rise up again; but the wicked shall stumble into misfortune.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
At the fall of thy enemy do not rejoice; and at his stumbling let not thy heart be glad:
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Lest the Lord see it and it be displeasing in his eyes, and he turn away from him his wrath.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Fret not thyself because of evil-doers, neither be thou envious of the wicked;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For there will be no [happy] future for the bad man: the lamp of the wicked will be quenched.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
My son, fear the Lord and the king: with those that are desirous to change do not mingle thyself;
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
For suddenly will their calamity arise; and who knoweth the ruin of both of them!
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
These things also are for the wise. To have respect of persons in judgment is not good.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Him that saith unto the wicked, Thou art righteous, will the people denounce, him will nations hold accursed;
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
But to those that punish delight shall be given, and upon them shall come the blessing of the good.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Men will kiss the lips of him that giveth a proper answer.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare without thy work, and make it fit in the field for thyself: and afterward build thy house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Be not without cause a witness against thy neighbor; for wouldst thou beguile with thy lips?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Say not, As he hath done to me so will I do to him: I will recompense every man according to his doing.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
By the field of a slothful man I once passed along, and by the vineyard of a man void of sense:
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
And, lo, it was all grown over with thorns, nettles had covered its surface, and its stone-wall was broken down.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
And when I had indeed beheld [this] I took it to my heart: I saw it, and received a warning.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
“A little [more] sleep, a little slumber, a little folding of the hands in lying down;”
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
But then will thy poverty come like a rover; and thy wants as a man armed with a shield.