< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Be not thou envious against evil men, neither desire to be with them.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
For their heart studieth destruction, and their lips talk of mischief.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Through wisdom is an house builded; and by understanding it is established:
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
And by knowledge shall the chambers be filled with all precious and pleasant riches.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
A wise man is strong; yea, a man of knowledge increaseth strength.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
For by wise counsel thou shalt make thy war: and in multitude of counsellers there is safety.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdom is too high for a fool: he openeth not his mouth in the gate.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
He that deviseth to do evil shall be called a mischievous person.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The thought of foolishness is sin: and the scorner is an abomination to men.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
If thou faint in the day of adversity, thy strength is small.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
If thou forbear to deliver them that are drawn unto death, and those that are ready to be slain;
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
If thou sayest, Behold, we knew it not; doth not he that pondereth the heart consider it? and he that keepeth thy soul, doth not he know it? and shall not he render to every man according to his works?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
My son, eat thou honey, because it is good; and the honeycomb, which is sweet to thy taste:
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
So shall the knowledge of wisdom be unto thy soul: when thou hast found it, then there shall be a reward, and thy expectation shall not be cut off.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Lay not wait, O wicked man, against the dwelling of the righteous; spoil not his resting place:
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For a just man falleth seven times, and riseth up again: but the wicked shall fall into mischief.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Rejoice not when thine enemy falleth, and let not thine heart be glad when he stumbleth:
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Lest YHWH see it, and it displease him, and he turn away his wrath from him.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Fret not thyself because of evil men, neither be thou envious at the wicked;
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For there shall be no reward to the evil man; the candle of the wicked shall be put out.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
My son, fear thou YHWH and the king: and meddle not with them that are given to change:
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
For their calamity shall rise suddenly; and who knoweth the ruin of them both?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
These things also belong to the wise. It is not good to have respect of persons in judgment.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
He that saith unto the wicked, Thou are righteous; him shall the people curse, nations shall abhor him:
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
But to them that rebuke him shall be delight, and a good blessing shall come upon them.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Every man shall kiss his lips that giveth a right answer.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare thy work without, and make it fit for thyself in the field; and afterwards build thine house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Be not a witness against thy neighbour without cause; and deceive not with thy lips.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Say not, I will do so to him as he hath done to me: I will render to the man according to his work.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
I went by the field of the slothful, and by the vineyard of the man void of understanding;
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
And, lo, it was all grown over with thorns, and nettles had covered the face thereof, and the stone wall thereof was broken down.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Then I saw, and considered it well: I looked upon it, and received instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Yet a little sleep, a little slumber, a little folding of the hands to sleep:
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
So shall thy poverty come as one that travelleth; and thy want as an armed man.

< Karin Magana 24 >