< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Be not thou enuious against euill men, neither desire to be with them.
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
For their heart imagineth destruction, and their lippes speake mischiefe.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Through wisdome is an house builded, and with vnderstanding it is established.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
And by knowledge shall the chambers bee filled with all precious, and pleasant riches.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
A wise man is strong: for a man of vnderstanding encreaseth his strength.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
For with counsel thou shalt enterprise thy warre, and in the multitude of them that can giue counsell, is health.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdome is hie to a foole: therefore he can not open his mouth in the gate.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Hee that imagineth to doe euill, men shall call him an autour of wickednes.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The wicked thought of a foole is sinne, and the scorner is an abomination vnto men.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
If thou bee faint in the day of aduersitie, thy strength is small.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Deliuer them that are drawen to death: wilt thou not preserue them that are led to be slaine?
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
If thou say, Beholde, we knew not of it: he that pondereth the heartes, doeth not hee vnderstand it? and hee that keepeth thy soule, knoweth he it not? will not he also recompense euery man according to his workes?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
My sonne, eate hony, for it is good, and the hony combe, for it is sweete vnto thy mouth.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
So shall the knowledge of wisdome be vnto thy soule, if thou finde it, and there shall be an ende, and thine hope shall not be cut off.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Laye no waite, O wicked man, against the house of the righteous, and spoyle not his resting place.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For a iust man falleth seuen times, and riseth againe: but the wicked fall into mischiefe.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Bee thou not glad when thine enemie falleth, and let not thine heart reioyce when hee stumbleth,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Least the Lord see it, and it displease him, and he turne his wrath from him.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Fret not thy selfe because of the malicious, neither be enuious at the wicked.
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For there shall bee none ende of plagues to the euill man: the light of the wicked shall bee put out.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
My sonne feare the Lord, and the King, and meddle not with them that are sedicious.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
For their destruction shall rise suddenly, and who knoweth the ruine of them both?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
ALSO THESE THINGS PERTEINE TO THE WISE, It is not good to haue respect of any person in iudgement.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
He that saith to the wicked, Thou art righteous, him shall the people curse, and the multitude shall abhorre him.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
But to them that rebuke him, shall be pleasure, and vpon them shall come the blessing of goodnesse.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
They shall kisse the lippes of him that answereth vpright wordes.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare thy worke without, and make readie thy thinges in the fielde, and after, builde thine house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Be not a witnes against thy neighbour without cause: for wilt thou deceiue with thy lippes?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Say not, I wil doe to him, as he hath done to mee, I will recompence euery man according to his worke.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
I passed by the fielde of the slouthfull, and by the vineyarde of the man destitute of vnderstanding.
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
And lo, it was al growen ouer with thornes, and nettles had couered the face thereof, and the stone wall thereof was broken downe.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Then I behelde, and I considered it well: I looked vpon it, and receiued instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Yet a litle sleepe, a litle slumber, a litle folding of the handes to sleepe.
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
So thy pouertie commeth as one that traueileth by the way, and thy necessitie like an armed man.

< Karin Magana 24 >