< Karin Magana 23 >

1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
CUANDO te sentares á comer con algún señor, considera bien lo que estuviere delante de ti;
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
Y pon cuchillo á tu garganta, si tienes gran apetito.
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
No codicies sus manjares delicados, porque es pan engañoso.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
No trabajes por ser rico; pon coto á tu prudencia.
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
¿Has de poner tus ojos en las riquezas, siendo ningunas? porque hacerse han alas, como alas de águila, y volarán al cielo.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
No comas pan de [hombre de] mal ojo, ni codicies sus manjares:
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
Porque cual es su pensamiento en su alma, tal es él. Come y bebe, te dirá; mas su corazón no está contigo.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
Vomitarás la parte que tú comiste, y perderás tus suaves palabras.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
No hables á oídos del necio; porque menospreciará la prudencia de tus razones.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
No traspases el término antiguo, ni entres en la heredad de los huérfanos:
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
Porque el defensor de ellos es el Fuerte, el cual juzgará la causa de ellos contra ti.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Aplica tu corazón á la enseñanza, y tus oídos á las palabras de sabiduría.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
No rehuses la corrección del muchacho: [porque] si lo hirieres con vara, no morirá.
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
Tú lo herirás con vara, y librarás su alma del infierno. (Sheol h7585)
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
Hijo mío, si tu corazón fuere sabio, también á mí se me alegrará el corazón;
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
Mis entrañas también se alegrarán, cuando tus labios hablaren cosas rectas.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
No tenga tu corazón envidia de los pecadores, antes [persevera] en el temor de Jehová todo tiempo:
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Porque ciertamente hay fin, y tu esperanza no será cortada.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Oye tú, hijo mío, y sé sabio, y endereza tu corazón al camino.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
No estés con los bebedores de vino, ni con los comedores de carne:
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
Porque el bebedor y el comilón empobrecerán: y el sueño hará vestir vestidos rotos.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Oye á tu padre, á aquel que te engendró; y cuando tu madre envejeciere, no la menosprecies.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Compra la verdad, y no la vendas; la sabiduría, la enseñanza, y la inteligencia.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
Mucho se alegrará el padre del justo: y el que engendró sabio se gozará con él.
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
Alégrense tu padre y tu madre, y gócese la que te engendró.
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
Dame, hijo mío, tu corazón, y miren tus ojos por mis caminos.
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
Porque sima profunda es la ramera, y pozo angosto la extraña.
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
También ella, como robador, acecha, y multiplica entre los hombres los prevaricadores.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
¿Para quién será el ay? ¿para quién el ay? ¿para quién las rencillas? ¿para quién las quejas? ¿para quién las heridas en balde? ¿para quién lo amoratado de los ojos?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
Para los que se detienen mucho en el vino, para los que van buscando la mistura.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
No mires al vino cuando rojea, cuando resplandece su color en el vaso: éntrase suavemente;
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
[Mas] al fin como serpiente morderá, y como basilisco dará dolor:
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
Tus ojos mirarán las extrañas, y tu corazón hablará perversidades.
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
Y serás como el que yace en medio de la mar, ó como el que está en la punta de un mastelero.
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
[Y dirás]: Hiriéronme, mas no me dolió; azotáronme, mas no lo sentí; cuando despertare, aun lo tornaré á buscar.

< Karin Magana 23 >