< Karin Magana 23 >
1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
Cuando te sientas a comer con uno de los grandes, mira con atención lo que te ponen delante;
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
y aplica un cuchillo a tu garganta, si eres un hombre de gran apetito.
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
No muestres avidez de sus delicadas viandas, pues son un manjar engañoso.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
No te afanes por ganar riquezas; pon coto a tus deseos.
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
No fijes tus ojos en las (riquezas) perecederas, pues ellas se toman alas, como de águila y vuelan hacia el cielo.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
No comas pan con el envidioso; no codicies sus delicados manjares;
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
porque así como los pensamientos de su alma es él. “Come y bebe”, te dice; mas su corazón no está contigo.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
Vomitarás el bocado que comiste, y habrás desperdiciado tus amables palabras.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
No hables a los oídos del necio, pues despreciará tus sabios razonamientos.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
No trasplantes los hitos antiguos, ni pongas tu pie en los campos de los huérfanos.
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
Porque su vengador es fuerte; Él tomará contra ti la causa de ellos.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Aplica tu corazón a la instrucción, y tus oídos a los dichos de la sabiduría.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
No ahorres al joven la corrección; puesto que no morirá aunque le castigues con la vara.
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
Si lo castigas con la vara, librarás su alma del scheol. (Sheol )
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
Hijo mío, si tu corazón es sabio, se alegrará mi corazón;
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
y se regocijarán mis entrañas cuando tus labios hablen de cosas rectas.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
No envidie tu corazón a los pecadores, antes (persevera) en el temor de Yahvé en todo tiempo.
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Porque hay cosas venideras, y tu esperanza no quedará burlada.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Escúchame, hijo mío, y sé sabio, endereza tu corazón por la (recta) senda.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
No seas compañero de los bebedores de vino, ni de los que comen carne sin medida.
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
Porque los que beben y comen sin medida, se empobrecen; y la somnolencia los lleva a vestir andrajos.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Escucha a tu padre que te engendró; y no desprecies a tu madre cuando envejeciere.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Adquiere la verdad, y no la vendas, tampoco la sabiduría, la doctrina e inteligencia.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
Salta de placer el padre del justo, y el que engendra a un sabio tendrá en él su gozo.
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
¡Alégrense, pues, tu padre y tu madre; regocíjese la que te dio a luz!
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
Dame, hijo mío, tu corazón, y tus ojos tengan placer en mis caminos;
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
porque fosa honda es la ramera, y pozo angosto la mujer ajena.
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
También ella, como un salteador, está al acecho, y aumenta el número de los prevaricadores entre los hombres.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
¿Para quién los ayes? ¿Para quién los lamentos? ¿Para quién las riñas? ¿Para quién las querellas? ¿Para quién las heridas sin motivo? ¿Para quién los ojos hinchados?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
Son para los que no pueden separarse del vino, para los que andan en busca de vino aromático.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
No mires el vino cómo rojea; cómo en la copa se refleja su color; ni cómo fluye suavemente.
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
Porque al fin muerde como una serpiente, y pica cual basilisco.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
Tus ojos irán tras mujeres extrañas, y tu corazón hablará cosas perversas.
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
Serás como un hombre que se acuesta en medio del mar, y duerme sobre la punta de un mástil.
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
(Dirás): “Me han apaleado, y no me duele, me han golpeado, y nada siento. Cuando me despierte volveré a tomar de nuevo.”