< Karin Magana 23 >

1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
Wenn du dich hinsetzest, um mit einem Herrscher zu speisen, so beachte wohl, wen du vor dir hast;
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
und setze ein Messer an deine Kehle, wenn du gierig bist.
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
Laß dich nicht gelüsten nach seinen Leckerbissen, denn sie sind eine trügliche Speise.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
Bemühe dich nicht, reich zu werden, laß ab von deiner Klugheit.
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
Willst du deine Augen darauf hinfliegen lassen, und siehe, fort ist es? Denn sicherlich schafft es sich Flügel gleich dem Adler, der gen Himmel fliegt.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
Iß nicht das Brot des Scheelsehenden, und laß dich nicht gelüsten nach seinen Leckerbissen.
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
Denn wie er es abmißt in seiner Seele, so ist er. “Iß und trink!”, spricht er zu dir, aber sein Herz ist nicht mit dir.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
Deinen Bissen, den du gegessen hast, mußt du ausspeien, und deine freundlichen Worte wirst du verlieren.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
Rede nicht zu den Ohren eines Toren, denn er wird die Einsicht deiner Worte verachten.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
Verrücke nicht die alte Grenze, und dringe nicht ein in die Felder der Waisen.
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
Denn ihr Erlöser ist stark; er wird ihren Rechtsstreit wider dich führen.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Bringe dein Herz her zur Unterweisung, und deine Ohren zu den Worten der Erkenntnis.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
Entziehe dem Knaben nicht die Züchtigung; wenn du ihn mit der Rute schlägst, wird er nicht sterben.
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
Du schlägst ihn mit der Rute, und du errettest seine Seele von dem Scheol. (Sheol h7585)
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
Mein Sohn, wenn dein Herz weise ist, so wird auch mein Herz sich freuen;
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
und meine Nieren werden frohlocken, wenn deine Lippen Geradheit reden.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
Dein Herz beneide nicht die Sünder, sondern beeifere sich jeden Tag um die Furcht Jehovas.
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Wahrlich, es gibt ein Ende, und deine Hoffnung wird nicht vernichtet werden.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Höre du, mein Sohn, und werde weise, und leite dein Herz geradeaus auf dem Wege.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
Sei nicht unter Weinsäufern, noch unter denen, die Fleisch verprassen;
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
denn ein Säufer und ein Schlemmer verarmen, und Schlummer kleidet in Lumpen.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Höre auf deinen Vater, der dich gezeugt hat, und verachte deine Mutter nicht, wenn sie alt geworden ist.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Kaufe Wahrheit und verkaufe sie nicht, Weisheit und Unterweisung und Verstand.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
Hoch frohlockt der Vater eines Gerechten; und wer einen Weisen gezeugt hat, der freut sich seiner.
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
Freuen mögen sich dein Vater und deine Mutter, und frohlocken, die dich geboren!
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
Gib mir, mein Sohn, dein Herz, und laß deine Augen Gefallen haben an meinen Wegen!
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
Denn die Hure ist eine tiefe Grube und die Fremde ein enger Brunnen;
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
ja, sie lauert auf wie ein Räuber, und sie mehrt die Treulosen unter den Menschen.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
Wer hat Ach, wer hat Weh, wer Zänkereien, wer Klage, wer Wunden ohne Ursache? Wer Trübung der Augen?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
Die spät beim Weine sitzen, die einkehren, um Mischtrank zu kosten.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
Sieh den Wein nicht an, wenn er sich rot zeigt, wenn er im Becher blinkt, leicht hinuntergleitet.
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
Sein Ende ist, daß er beißt wie eine Schlange und sticht wie ein Basilisk.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
Deine Augen werden Seltsames sehen, und dein Herz wird verkehrte Dinge reden.
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
Und du wirst sein wie einer, der im Herzen des Meeres liegt, und wie einer, der da liegt auf der Spitze eines Mastes.
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
“Man hat mich geschlagen, es schmerzte mich nicht; man hat mich geprügelt, ich fühlte es nicht. Wann werde ich aufwachen? Ich will es wieder tun, will ihn abermals aufsuchen.”

< Karin Magana 23 >