< Karin Magana 23 >

1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
When thou sittest to eat with a ruler, thou shalt consider well, what is before thee;
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
And shalt put a knife to thy throat, if, of great appetite, thou art:
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
Do not crave his dainties, for, the same, are deceitful food.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
Do not toil to get wealth, of thine own understanding, forbear:
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
Wilt thou let thine eye fly thereupon, when it is nothing? for it will, surely make, itself wings, Like an eagle, will it wing its way across the heavens.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
Do not eat the food of him that hath a begrudging eye, neither crave thou his dainties;
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
For, just as he hath thought in his own mind, so, he is: Eat and drink! he may say to thee, but, his heart, is not with thee.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
As for thy morsel thou hast eaten, thou shalt vomit it, so shalt thou waste thy things so sweet.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
In the ears of a dullard, do not speak, for he will despise the good sense of thy words.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
Do not move back the ancient boundary, and, into the fields of the fatherless, do not enter;
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
For, their near of kin, is strong, he, will plead their cause with thee.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Bring, to correction, thy heart, and thine ears, to the sayings of knowledge.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
Do not withhold, from a child, correction, When thou smitest him with the rod, he shall not die:
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
Thou, with the rod, shalt smite him, and, his soul from hades, shalt thou deliver. (Sheol h7585)
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
My son! if thy heart be wise, my heart shall rejoice, even mine.
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
So shall my reins exult, when thy lips speak the things that are right.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
Let not thy heart be envious of sinners, only of the reverence of Yahweh, all day long;
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
For surely there is a future, and, thine expectation, shall not be cut off.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Hear, thou, my son, and be wise, and lead forward, in duty, thy heart.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
Do not be among them who tipple with wine, —among them who are gluttons;
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
For, the tippler and the glutton, shall come to poverty, and, rags, shall Slumber put on!
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Hearken to thy father here, who begat thee, and despise not, when she is old, thy mother.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Truth, buy thou, but do not sell, wisdom, and correction, and understanding.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
Greatly shall exult, the father of a righteous man, and, he that begetteth a wise son, shall rejoice in him:
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
Rejoice shall thy father and thy mother, yea she, shall exult, who bare thee.
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
Oh give, my son, thy mind unto me, and let, thine eyes, observe, my ways;
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
For, a deep chasm, is the unchaste woman, and, a narrow pit, the female unknown;
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
Yea, she, as for prey, lieth in wait, and, the treacherous among mankind, she causeth to abound.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
Who hath woe? Who hath outcry of pain? Who hath contentions? Who hath complaining? Who hath needless wounds? Who hath dullness of eyes?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
They who tarry over wine, they who go in to search for mixed wine.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
Do not look on wine when it becometh red, when it giveth in the cup its sparkle, glideth down smoothly.
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
Its after effect, is that, like a serpent, it biteth, and, like a viper, it doth sting.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
Thine eyes, will see strange women, and, thy heart, will speak perverse things:
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
So shalt thou become, as one lying down in the heart of the sea, —or as one lying down on the top of the mastgear:
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
They smote me—I felt no pain, They struck me down—I noticed it not, —When shall I wake up? I will go on, I will seek it, again!

< Karin Magana 23 >