< Karin Magana 23 >

1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
When thou sittest to eat with a ruler, Consider well what is before thee;
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
For thou wilt put a knife to thy throat, If thou art a man given to appetite!
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
Long not for his dainties. For they are deceitful meat.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
Toil not to become rich; Cease from this, thy wisdom.
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
Wilt thou let thine eyes fly toward them? They are gone! For riches truly make to themselves wings; They fly away like the eagle toward heaven.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
Eat not the bread of him that hath an evil eye, And long not for his dainties;
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
For as he thinketh in his heart, so is he. “Eat and drink!” saith he to thee; But his heart is not with thee.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
The morsel, which thou hast eaten, thou shalt vomit up; And thou wilt have thrown away thy sweet words.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
Speak not in the ears of a fool; For he will despise the wisdom of thy words.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
Remove not the ancient landmark, And enter not into the fields of the fatherless!
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
For their avenger is mighty; He will maintain their cause against thee.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Apply thy heart to instruction, And thine ears to the words of knowledge.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
Withhold not correction from a child; If thou beat him with the rod, he will not die.
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
Beat him thyself with the rod, And thou shalt rescue him from the underworld. (Sheol h7585)
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
My son, if thy heart be wise, My heart shall rejoice, even mine;
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
Yea, my reins shall exult, When thy lips speak right things.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
Let not thy heart envy sinners, But continue thou in the fear of the LORD all the day long;
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
For surely there shall be a reward, And thine expectation shall not be cut off.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Hear thou, my son, and be wise; And let thy heart go forward in the way!
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
Be not thou among winebibbers, And riotous eaters of flesh;
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
For the drunkard and the glutton shall come to poverty, And drowsiness will clothe a man with rags.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Hearken to thy father, who begat thee, And despise not thy mother when she is old.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Buy the truth, and sell it not; Buy wisdom and instruction and understanding.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
The father of a righteous man shall greatly rejoice; Yea, he who begetteth a wise child shall have joy in him.
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
Let thy father and thy mother have joy; Yea, let her that bore thee rejoice!
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
My son, give me thy heart, And let thine eyes observe my ways!
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
For a harlot is a deep ditch; Yea, a strange woman is a narrow pit.
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
Like a robber she lieth in wait, And increaseth the treacherous among men.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
Who hath woe? Who hath sorrow? Who contentions? Who anxiety? Who wounds without cause? Who dimness of eyes?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
They that tarry long at the wine; They that go in to seek mixed wine.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
Look not thou upon the wine when it is red, When it sparkleth in the cup, When it goeth down smoothly.
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
At the last it biteth like a serpent, And stingeth like an adder.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
Thine eyes will look upon strange women, And thy heart will utter perverse things.
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
Yea, thou shalt be as one that lieth down in the midst of the sea, And as one that lieth down upon the top of a mast.
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
They have stricken me [[shalt thou say]], —I suffered no pain! They have beaten me, —I felt it not! When shall I awake? I will seek it yet again.

< Karin Magana 23 >