< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
DE más estima es la buena fama que las muchas riquezas; y la buena gracia más que la plata y el oro.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
El rico y el pobre se encontraron: á todos ellos hizo Jehová.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
El avisado ve el mal, y escóndese: mas los simples pasan, y reciben el daño.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Riquezas, y honra, y vida, [son] la remuneración de la humildad [y] del temor de Jehová.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Espinas [y] lazos hay en el camino del perverso: el que guarda su alma se alejará de ellos.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Instruye al niño en su carrera: aun cuando fuere viejo no se apartará de ella.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
El rico se enseñoreará de los pobres; y el que toma prestado, siervo es del que empresta.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
El que sembrare iniquidad, iniquidad segará: y consumiráse la vara de su ira.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
El ojo misericordioso será bendito, porque dió de su pan al indigente.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Echa fuera al escarnecedor, y saldrá la contienda, y cesará el pleito y la afrenta.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
El que ama la limpieza de corazón, [por] la gracia de sus labios su amigo será el rey.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Los ojos de Jehová miran por la ciencia; mas él trastorna las cosas de los prevaricadores.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Dice el perezoso: El león está fuera; en mitad de las calles seré muerto.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
Sima profunda es la boca de las extrañas: aquel contra el cual estuviere Jehová airado, caerá en ella.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La necedad está ligada en el corazón del muchacho; [mas] la vara de la corrección la hará alejar de él.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
El que oprime al pobre para aumentarse él, y que da al rico, ciertamente [será] pobre.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Inclina tu oído, y oye las palabras de los sabios, y pon tu corazón á mi sabiduría:
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Porque es cosa deleitable, si las guardares en tus entrañas; y que juntamente sean ordenadas en tus labios.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Para que tu confianza sea en Jehová, te [las] he hecho saber hoy á ti también.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
¿No te he escrito tres veces en consejos y ciencia,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
Para hacerte saber la certidumbre de las razones verdaderas, para que puedas responder razones de verdad á los que á ti enviaren?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
No robes al pobre, porque es pobre, ni quebrantes en la puerta al afligido:
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Porque Jehová juzgará la causa de ellos, y despojará el alma de aquellos que los despojaren.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
No te entrometas con el iracundo, ni te acompañes con el hombre de enojos;
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
Porque no aprendas sus maneras, y tomes lazo para tu alma.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
No estés entre los que tocan la mano, entre los que fían por deudas.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Si no tuvieres para pagar, ¿por qué han de quitar tu cama de debajo de ti?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
No traspases el término antiguo que pusieron tus padres.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
¿Has visto hombre solícito en su obra? delante de los reyes estará; no estará delante de los de baja suerte.