< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
El buen nombre es más deseable que las grandes riquezas, y el favor amoroso es mejor que la plata y el oro.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Los ricos y los pobres tienen esto en común: Yahvé es el creador de todos ellos.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
Un hombre prudente ve el peligro y se esconde; pero los simples pasan, y sufren por ello.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
El resultado de la humildad y el temor a Yahvé es la riqueza, el honor y la vida.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Espinas y trampas hay en el camino de los malvados; quien guarda su alma se aleja de ellos.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Educa al niño en el camino que debe seguir, y cuando sea viejo no se apartará de él.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Los ricos dominan a los pobres. El prestatario está al servicio del prestamista.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
El que siembra maldad cosecha problemas, y la vara de su furia será destruida.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
El que tiene un ojo generoso será bendecido, porque comparte su comida con los pobres.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Expulsa al burlón, y se acabará la contienda; sí, se acabarán las peleas y los insultos.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
El que ama la pureza de corazón y habla con gracia es el amigo del rey.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Los ojos de Yahvé vigilan el conocimiento, pero frustra las palabras de los infieles.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
El perezoso dice: “¡Hay un león afuera! Me matarán en las calles”.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
La boca de una adúltera es un pozo profundo. El que está bajo la ira de Yahvé caerá en ella.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La locura está ligada al corazón de un niño; la vara de la disciplina lo aleja de él.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
El que oprime al pobre para su propio aumento y el que da al rico, ambos llegan a la pobreza.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Vuelve tu oído y escucha las palabras de los sabios. Aplica tu corazón a mis enseñanzas.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Porque es una cosa agradable si las guardas dentro de ti, si todos ellos están listos en sus labios.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Hoy te enseño, incluso a ti, para que tu confianza esté en Yahvé.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
¿No te he escrito treinta cosas excelentes de consejo y conocimiento,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
Para enseñarte la verdad, palabras fiables, para dar respuestas sólidas a los que te enviaron?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
No exploten al pobre porque es pobre; y no aplastar a los necesitados en los tribunales;
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
porque Yahvé defenderá su caso, y saquean la vida de los que los saquean.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
No te hagas amigo de un hombre de mal genio. No te asocies con quien alberga ira,
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
para que no aprendas sus caminos y atrapar tu alma.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
No seas de los que golpean las manos, de los que son garantía de las deudas.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Si no tienes medios para pagar, ¿por qué debería quitarte la cama de debajo de ti?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
No muevas el antiguo mojón que sus padres han establecido.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
¿Has visto hombre diligente en su obra? Estará delante de los reyes y no de la gentuza.