< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
É preferível ter um [bom] nome do que muitas riquezas; e ser favorecido é melhor que a prata e o o ouro.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
O rico e o pobre se encontram; todos eles foram feitos pelo SENHOR.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
O prudente vê o mal, e se esconde; mas os ingênuos passam e sofrem as consequências.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
A recompensa da humildade [e do] temor ao SENHOR são riquezas, honra, e vida.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
[Há] espinhos e ciladas no caminho do perverso; quem cuida de sua alma deve ficar longe de [tal caminho].
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Instrui ao menino em seu caminho, e até quando envelhecer, não se desviará dele.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
O rico domina sobre os pobres, e quem toma emprestado é servo daquele que empresta.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Aquele que semeia perversidade colherá sofrimento; e a vara de sua ira se acabará.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
Quem tem olhos bondosos será abençoado, porque deu de seu pão ao pobre.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Expulsa ao zombador, e a briga terminará; cessará a disputa e a vergonha.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Quem ama a pureza do coração [fala] graciosamente com os lábios, [e] o rei [será] seu amigo.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Os olhos do SENHOR protegem o conhecimento; porém ele transtornará as palavras do enganador.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
O preguiçoso diz: Há um leão lá fora! Ele me matará nas ruas!
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
A boca da mulher pervertida é uma cova profunda; aquele contra quem o SENHOR se irar cairá nela.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
A tolice está amarrada ao coração do menino; [mas] a vara da correção a mandará para longe dele.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Aquele que oprime ao pobre para proveito próprio e aquele que dá [suborno] ao rico certamente empobrecerão.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Inclina o teu ouvido e escuta as palavras dos sábios; dispõe teu coração ao meu conhecimento;
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
porque é agradável que as guardes dentro de ti, e estejam prontas para os teus lábios;
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
para que tua confiança esteja no SENHOR, eu as ensino a ti hoje.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Por acaso não te escrevi excelentes coisas sobre o conselho e o conhecimento,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
para te ensinar a certeza das palavras da verdade, para que possas responder palavras de verdade aos que te enviarem?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Não roubes ao pobre, porque ele é pobre; nem oprimas ao aflito junto à porta do julgamento.
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Porque o SENHOR defenderá a causa deles em juízo, e quanto aos que os roubam, ele lhes roubará a alma.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Não seja companheiro de quem se irrita facilmente, nem andes com o homem furioso,
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
Para que não aprendas o caminho dele, e te ponhas em armadilhas para tua alma.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Não estejas entre os que se comprometem em acordos com as mãos, [ou] os que ficam por fiadores de dívidas.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Se não tens como pagar, por que razão tirariam tua cama debaixo de ti?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Não mudes os limites antigos que teus pais fizeram.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Viste um homem habilidoso em sua obra? Perante a face dos reis ele será posto; ele não será posto diante de pessoas sem honra.

< Karin Magana 22 >