< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
melius est nomen bonum quam divitiae multae super argentum et aurum gratia bona
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
dives et pauper obviaverunt sibi utriusque operator est Dominus
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
callidus vidit malum et abscondit se innocens pertransiit et adflictus est damno
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
finis modestiae timor Domini divitiae et gloria et vita
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
arma et gladii in via perversi custos animae suae longe recedit ab eis
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
proverbium est adulescens iuxta viam suam etiam cum senuerit non recedet ab ea
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
dives pauperibus imperat et qui accipit mutuum servus est fenerantis
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
qui seminat iniquitatem metet mala et virga irae suae consummabitur
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
qui pronus est ad misericordiam benedicetur de panibus enim suis dedit pauperi
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
eice derisorem et exibit cum eo iurgium cessabuntque causae et contumeliae
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
qui diligit cordis munditiam propter gratiam labiorum suorum habebit amicum regem
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
oculi Domini custodiunt scientiam et subplantantur verba iniqui
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
dicit piger leo foris in medio platearum occidendus sum
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
fovea profunda os alienae cui iratus est Dominus incidet in eam
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
stultitia conligata est in corde pueri et virga disciplinae fugabit eam
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
qui calumniatur pauperem ut augeat divitias suas dabit ipse ditiori et egebit
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
inclina aurem tuam et audi verba sapientium adpone autem cor ad doctrinam meam
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
quae pulchra erit tibi cum servaveris eam in ventre tuo et redundabit in labiis tuis
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
ut sit in Domino fiducia tua unde et ostendi eam tibi hodie
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
ecce descripsi eam tibi tripliciter in cogitationibus et scientia
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
ut ostenderem tibi firmitatem et eloquia veritatis respondere ex his illi qui misit te
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
non facias violentiam pauperi quia pauper est neque conteras egenum in porta
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
quia Dominus iudicabit causam eius et configet eos qui confixerint animam eius
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
noli esse amicus homini iracundo neque ambules cum viro furioso
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
ne forte discas semitas eius et sumas scandalum animae tuae
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
noli esse cum his qui defigunt manus suas et qui vades se offerunt pro debitis
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
si enim non habes unde restituas quid causae est ut tollat operimentum de cubili tuo
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
ne transgrediaris terminos antiquos quos posuerunt patres tui
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
vidisti virum velocem in opere suo coram regibus stabit nec erit ante ignobiles