< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
La renommée est préférable aux grandes richesses, et la bonne grâce plus que l'argent ni l'or.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Le riche et le pauvre s'entre-rencontrent: celui qui les a tous faits, c'est l'Eternel.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
L'homme bien avisé prévoit le mal, et se tient caché; mais les niais passent, et en payent l'amende.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
La récompense de la débonnaireté et de la crainte de l'Eternel sont les richesses, la gloire et la vie.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Il y a des épines et des pièges dans la voie du pervers; celui qui aime son âme, s'en retirera loin.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Instruis le jeune enfant, à l'entrée de sa voie; lors même qu'il sera devenu vieux, il ne s'en retirera point.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Le riche dominera sur les pauvres; et celui qui emprunte, sera serviteur de l'homme qui prête.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Celui qui sème la perversité, moissonnera le tourment; et la verge de son indignation prendra fin.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
L'œil bénin sera béni, parce qu'il aura donné de son pain au pauvre.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Chasse le moqueur, et le débat sortira, et la querelle, et l'ignominie cesseront.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Le Roi est ami de celui qui aime la pureté de cœur, et qui a de la grâce en son parler.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Les yeux de l'Eternel protègent la science, mais il renverse les paroles du perfide.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Le paresseux dit: le lion est là dehors; je serais tué dans les rues.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
La bouche des étrangers est une fosse profonde; celui que l'Eternel a en détestation, y tombera.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La folie est liée au cœur du jeune enfant; [mais] la verge du châtiment la fera éloigner de lui.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Celui qui fait tort au pauvre pour s'accroître, et qui donne au riche, ne peut manquer de tomber dans l'indigence.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Prête ton oreille, et écoute les paroles des sages, et applique ton cœur à ma science.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Car ce te sera une chose agréable si tu les gardes au-dedans de toi, et si elles sont rangées ensemble sur tes lèvres.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Je te l'ai aujourd'hui fait entendre, à toi, dis-je, afin que ta confiance soit en l'Eternel.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Ne t'ai-je pas écrit des choses convenables aux Gouverneurs en conseil et en science;
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
Afin de te donner à connaître la certitude des paroles de vérité, pour répondre des paroles de vérité à ceux qui envoient vers toi?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Ne pille point le chétif, parce qu'il est chétif; et ne foule point l'affligé à la porte.
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Car l'Eternel défendra leur cause, et enlèvera l'âme de ceux qui les auront volés.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Ne t'accompagne point de l'homme colère, et ne va point avec l'homme furieux;
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
De peur que tu n'apprennes son train, et que tu ne reçoives un piège dans ton âme.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Ne sois point de ceux qui frappent dans la main, ni de ceux qui cautionnent pour les dettes.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Si tu n'avais pas de quoi payer, pourquoi prendrait-on ton lit de dessous toi?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Ne recule point la borne ancienne que tes pères ont faite.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
As-tu vu un homme habile en son travail? il sera au service des Rois, et non à celui des gens de basse condition.

< Karin Magana 22 >