< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
La réputation est préférable à de grandes richesses, Et la grâce vaut mieux que l’argent et que l’or.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Le riche et le pauvre se rencontrent; C’est l’Éternel qui les a faits l’un et l’autre.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
L’homme prudent voit le mal et se cache, Mais les simples avancent et sont punis.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Le fruit de l’humilité, de la crainte de l’Éternel, C’est la richesse, la gloire et la vie.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Des épines, des pièges sont sur la voie de l’homme pervers; Celui qui garde son âme s’en éloigne.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Instruis l’enfant selon la voie qu’il doit suivre; Et quand il sera vieux, il ne s’en détournera pas.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Le riche domine sur les pauvres, Et celui qui emprunte est l’esclave de celui qui prête.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Celui qui sème l’iniquité moissonne l’iniquité, Et la verge de sa fureur disparaît.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
L’homme dont le regard est bienveillant sera béni, Parce qu’il donne de son pain au pauvre.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Chasse le moqueur, et la querelle prendra fin; Les disputes et les outrages cesseront.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Celui qui aime la pureté du cœur, Et qui a la grâce sur les lèvres, a le roi pour ami.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Les yeux de l’Éternel gardent la science, Mais il confond les paroles du perfide.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Le paresseux dit: Il y a un lion dehors! Je serai tué dans les rues!
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
La bouche des étrangères est une fosse profonde; Celui contre qui l’Éternel est irrité y tombera.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La folie est attachée au cœur de l’enfant; La verge de la correction l’éloignera de lui.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Opprimer le pauvre pour augmenter son bien, C’est donner au riche pour n’arriver qu’à la disette.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Prête l’oreille, et écoute les paroles des sages; Applique ton cœur à ma science.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Car il est bon que tu les gardes au-dedans de toi, Et qu’elles soient toutes présentes sur tes lèvres.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Afin que ta confiance repose sur l’Éternel, Je veux t’instruire aujourd’hui, oui, toi.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
N’ai-je pas déjà pour toi mis par écrit Des conseils et des réflexions,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
Pour t’enseigner des choses sûres, des paroles vraies, Afin que tu répondes par des paroles vraies à celui qui t’envoie?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Ne dépouille pas le pauvre, parce qu’il est pauvre, Et n’opprime pas le malheureux à la porte;
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Car l’Éternel défendra leur cause, Et il ôtera la vie à ceux qui les auront dépouillés.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Ne fréquente pas l’homme colère, Ne va pas avec l’homme violent,
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
De peur que tu ne t’habitues à ses sentiers, Et qu’ils ne deviennent un piège pour ton âme.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Ne sois pas parmi ceux qui prennent des engagements, Parmi ceux qui cautionnent pour des dettes;
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Si tu n’as pas de quoi payer, Pourquoi voudrais-tu qu’on enlève ton lit de dessous toi?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Ne déplace pas la borne ancienne, Que tes pères ont posée.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Si tu vois un homme habile dans son ouvrage, Il se tient auprès des rois; Il ne se tient pas auprès des gens obscurs.

< Karin Magana 22 >