< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
Une bonne renommée vaut mieux que de grandes richesses; la bonne grâce vaut mieux que l'or et l'argent.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Le riche et le pauvre se sont rencontrés; c'est le Seigneur qui les a créé tous les deux.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
L'homme habile, en voyant le pervers sévèrement châtié, se corrige lui- même; les imprudents passent outre, et sont punis à leur tour.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
La crainte du Seigneur fait naître la sagesse, et les biens, et la gloire, et la vie.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Les chausse-trapes et les filets sont dans les voies tortueuses; mais celui qui garde son âme les évitera.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Les riches commanderont aux pauvres, et des serviteurs prêteront à usure à leurs propres maîtres.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Qui sème la méchanceté récoltera le malheur, et il recevra le châtiment de ses œuvres. Dieu bénit l'homme joyeux et libéral; mais le mauvais semeur sera puni par la vanité même de ses travaux.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
Celui qui a pitié des pauvres sera lui-même nourri; car il a donné de son pain au mendiant. Celui qui donne des présents se prépare victoire et honneur; mais il perd l'âme de ceux qui les acceptent.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Chassez de l'assemblée l'homme de pestilence; la discorde en sortira avec lui; car, lorsqu'il s'y assied, il la déshonore tout entière.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Le Seigneur aime les cœurs saints, et tous les innocents Lui sont agréables; un roi gouverne à la parole.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Les yeux du Seigneur surveillent la doctrine; le pervers méprise Sa parole.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Le paresseux apporte des excuses, et dit: Il y a un lion sur le chemin, et des assassins dans les rues.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
La bouche des méchants est un profond abîme; celui qui hait le Seigneur y tombera. Il y a devant l'homme des voies mauvaises, et il n'aime pas s'en détourner; cependant il est nécessaire d'éviter toute voie mauvaise et tortueuse.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La folie est attachée au cœur du jeune homme; la verge et la discipline sont loin de lui.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Celui qui trompe l'indigent augmente ses biens; mais il les diminue en faisant des présents au riche.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Incline ton oreille aux discours du sage; sois attentif à mes paroles; affermis ton cœur sur elles, afin que tu saches qu'elles sont bonnes.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Si tu les déposes en ton cœur, elles réjouiront ton cœur et tes lèvres.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Que ton espérance soit dans le Seigneur, et qu'Il te fasse connaître Sa voie.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Grave ces choses trois fois sur la face de ton cœur, afin de posséder la sagesse et la science.
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
C'est pour cela que je t'enseigne la parole véritable et la doctrine bonne à suivre, afin que tu répondes les paroles de la vérité à ceux qui se présenteront devant toi.
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Ne fais pas violence au pauvre, car il est dans le besoin; devant les portes de la ville, ne méprise point l'homme sans appui;
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
car le Seigneur Lui-même plaidera sa cause; et ainsi tu mettras ton âme en un sûr asile.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Ne sois pas le compagnon d'un orgueilleux; ne demeure pas avec un ami porté à la colère;
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
de peur que tu n'apprennes leurs voies, et que tu n'en reçoives des filets pour ton âme.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Ne t'engage pour personne, même par crainte de déplaire;
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
car si tu n'as pas de quoi payer, ils te prendront ta couverture sur les flancs.
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Ne déplaces pas les bornes que, de tout temps, les pères ont posées.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Il convient que l'homme clairvoyant et habile au travail s'approche des rois, mais non qu'il s'approche des pervers.