< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
Un nom estimé est préférable à la grande richesse: la sympathie est plus précieuse que l’argent et que l’or.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Riche et pauvre sont sur la même ligne: l’Eternel les a faits l’un et l’autre.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
L’Homme avisé aperçoit le danger et se met à l’abri; les niais passent outre et en pâtissent.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Fruits de l’humilité, de la crainte de Dieu: richesse, honneur et vie!
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Des lacets et des pièges sont semés sur la route du pervers; qui tient à sa vie s’en éloigne.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Donne au jeune homme de bonnes habitudes dès le début de sa carrière; même avancé en âge, il ne s’en écartera point.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Le riche prime les pauvres; le débiteur est prisonnier de son créancier.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Qui sème l’injustice, récolte l’adversité, l’instrument de sa passion sera anéanti.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
Celui qui a bon cœur sera béni, car il partage son pain avec le pauvre.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Expulse le persifleur, la discorde décampera avec lui, plus de disputes ni d’injures!
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Un ami au cœur pur, par l’agrément de ses lèvres, gagne l’affection du roi.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Les yeux de l’Eternel protègent le vrai savoir; mais ils renversent les entreprises du perfide.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Le paresseux s’écrie: "Il y a un lion dehors! Je vais être massacré en pleine rue!"
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
La bouche des femmes étrangères est comme un abîme profond; celui que Dieu réprouve y tombe.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
La sottise est attachée au cœur de l’adolescent; la verge qui châtie doit l’en arracher.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
On pressure le pauvre, et cela tourne à son profit; on donne au riche, et c’est un appauvrissement pour lui.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Incline ton oreille et écoute les paroles des sages; prête ton attention aux leçons de mon expérience.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
II sera beau pour toi de les retenir en ton cœur, de les fixer en permanence sur tes lèvres.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Mets ta confiance en l’Eternel; voilà ce que je t’enseigne à toi-même en ce jour.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
N’Est-ce pas à ton intention que j’ai consigné par écrit d’importantes maximes, en fait de bons conseils et d’expérience,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
pour t’apprendre ce qu’iI y a de réel dans les dictons de la vérité et te permettre de présenter fidèlement les choses à ceux qui t’envoient?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Ne dépouille pas le faible parce qu’il est sans défense; n’écrase pas le pauvre à la Porte,
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
car l’Eternel prend en mains leur cause et il traite avec rigueur ceux qui leur infligent des vexations.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Ne fraye pas avec un homme irascible, ne lie pas société avec quelqu’un qui s’emporte:
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
tu pourrais copier leurs mœurs et t’engager toi-même dans un piège.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Ne sois pas de ceux qui disent: "Touchez-là!" et qui se portent garants pour des emprunts.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Que tu n’aies pas de quoi payer, pourquoi t’exposer à ce que l’on saisisse la couche où tu reposes?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Ne déplace pas les bornes antiques, que tes pères ont posées.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Vois cet homme diligent dans son travail: il pourra paraître devant les rois au lieu de se tenir auprès des gens obscurs.