< Karin Magana 22 >
1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
Nimi on kalliimpi suurta rikkautta, suosio hopeata ja kultaa parempi.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Rikas ja köyhä kohtaavat toisensa; Herra on luonut kumpaisenkin.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
Mielevä näkee vaaran ja kätkeytyy, mutta yksinkertaiset käyvät kohti ja saavat vahingon.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Nöyryyden ja Herran pelon palkka on rikkaus, kunnia ja elämä.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Orjantappuroita ja pauloja on väärän tiellä; henkensä varjelee, joka niistä kaukana pysyy.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Totuta poikanen tiensä suuntaan, niin hän ei vanhanakaan siitä poikkea.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Rikas hallitsee köyhiä, ja velallinen joutuu velkojan orjaksi.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Joka vääryyttä kylvää, se turmiota niittää, ja hänen vihansa vitsa häviää.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
Hyvänsuopa saa siunauksen, sillä hän antaa leivästään vaivaiselle.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Aja pois pilkkaaja, niin poistuu tora ja loppuu riita ja häväistys.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Joka sydämen puhtautta rakastaa, jolla on suloiset huulet, sen ystävä on kuningas.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Herran silmät suojelevat taitoa, mutta uskottoman sanat hän kääntää väärään.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Laiska sanoo: "Ulkona on leijona; tappavat vielä minut keskellä toria".
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
Irstaitten vaimojen suu on syvä kuoppa; Herran vihan alainen kaatuu siihen.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
Hulluus on kiertynyt kiinni poikasen sydämeen, mutta kurituksen vitsa sen hänestä kauas karkoittaa.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Vaivaiselle on voitoksi, jos häntä sorretaan, rikkaalle tappioksi, jos hänelle annetaan.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Kallista korvasi ja kuuntele viisaitten sanoja ja tarkkaa minun taitoani.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Sillä suloista on, jos kätket ne sisimpääsi; olkoot ne kaikki huulillasi valmiina.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Että Herra olisi sinun turvanasi, siksi olen minä nyt neuvonut juuri sinua.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Olenhan ennenkin sinulle kirjoittanut, antanut neuvoja ja tietoa,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
opettaakseni sinulle totuutta, vakaita sanoja, että voisit vakain sanoin vastata lähettäjällesi.
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Älä raasta vaivaista, siksi että hän on vaivainen, äläkä polje kurjaa portissa,
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
sillä Herra ajaa hänen asiansa ja riistää hänen riistäjiltään hengen.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Älä rupea pikavihaisen ystäväksi äläkä seurustele kiukkuisen kanssa,
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
että et tottuisi hänen teihinsä ja saattaisi sieluasi ansaan.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Älä ole niitä, jotka kättä lyövät, jotka menevät takuuseen veloista.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
Jollei sinulla ole, millä maksaa, mitäs muuta, kuin viedään vuode altasi!
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Älä siirrä ikivanhaa rajaa, jonka esi-isäsi ovat asettaneet.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Jos näet miehen, kerkeän toimissaan, hänen paikkansa on kuningasten, ei alhaisten, palveluksessa.