< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
A [good] name is rather to be chosen than great riches, [And] loving favor rather than silver and gold.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
The rich and the poor meet together: Jehovah is the maker of them all.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
A prudent man seeth the evil, and hideth himself; But the simple pass on, and suffer for it.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
The reward of humility [and] the fear of Jehovah [Is] riches, and honor, and life.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Thorns [and] snares are in the way of the perverse: He that keepeth his soul shall be far from them.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Train up a child in the way he should go, And even when he is old he will not depart from it.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
The rich ruleth over the poor; And the borrower is servant to the lender.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
He that soweth iniquity shall reap calamity; And the rod of his wrath shall fail.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
He that hath a bountiful eye shall be blessed; For he giveth of his bread to the poor.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Cast out the scoffer, and contention will go out; Yea, strife and ignominy will cease.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
He that loveth pureness of heart, [For] the grace of his lips the king will be his friend.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
The eyes of Jehovah preserve [him that hath] knowledge; But he overthroweth the words of the treacherous man.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
The sluggard saith, There is a lion without; I shall be slain in the streets.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
The mouth of strange women is a deep pit; He that is abhorred of Jehovah shall fall therein.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
Foolishness is bound up in the heart of a child; [But] the rod of correction shall drive it far from him.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
He that oppresseth the poor to increase his [gain], [And] he that giveth to the rich, [shall come] only to want.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Incline thine ear, and hear the words of the wise, And apply thy heart unto my knowledge.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
For it is a pleasant thing if thou keep them within thee, If they be established together upon thy lips.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
That thy trust may be in Jehovah, I have made [them] known to thee this day, even to thee.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Have not I written unto thee excellent things Of counsels and knowledge,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
To make thee know the certainty of the words of truth, That thou mayest carry back words of truth to them that send thee?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Rob not the poor, because he is poor; Neither oppress the afflicted in the gate:
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
For Jehovah will plead their cause, And despoil of life those that despoil them.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Make no friendship with a man that is given to anger; And with a wrathful man thou shalt not go:
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
Lest thou learn his ways, And get a snare to thy soul.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Be thou not one of them that strike hands, [Or] of them that are sureties for debts.
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
If thou hast not wherewith to pay, Why should he take away thy bed from under thee?
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Remove not the ancient landmark, Which thy fathers have set.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Seest thou a man diligent in his business? he shall stand before kings; He shall not stand before mean men.

< Karin Magana 22 >