< Karin Magana 21 >
1 A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
Moyo wa mfalme ni mfereji wa maji katika mkono wa Yehova; anaugeuza popote anakopenda.
2 Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
Kila njia ya mtu ni sawa katika macho yake mwenyewe, lakini ni Yehova anayeipima mioyo.
3 Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
Kutenda haki na adili hukubaliwa zaidi na Yehova kuliko sadaka.
4 Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
Macho ya kiburi na moyo wa majivuno- taa ya waovu- ni dhambi.
5 Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
Mipango ya mwenye juhudi huelekea kwenye mafanikio tu, bali kila mtu anayetenda kwa haraka huelekea umasikini.
6 Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
Kujipatia utajiri kwa ulimi wa uongo ni mvuke unaopita upesi na mtego ambao unafisha.
7 Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
Vurugu ya waovu itawaburuta mbali, maana wanakataa kutenda haki.
8 Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
Njia ya mwenye hatia ni ukatiri, bali mwenye usafi hutenda yaliyo ya haki.
9 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Bora kuishi kwenye kona ya juu darini kuliko katika nyumba pamoja na mke mgonvi.
10 Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
Hamu ya mwovu ni uchu wa mabaya; jirani yake haoni ukarimu katika macho yake.
11 Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
Mwenye dhihaka anapoadhibiwa mjinga hupata busara, na mtu mwenye busara anapofundishwa, anaongeza maarifa.
12 Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
Atendaye haki huilinda nyumba ya mwovu; huwashusha waovu kwenye uharibifu.
13 In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
Anayeziba masikio yake kwenye kilio cha masikini, pia atalia, lakini hatajibiwa.
14 Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
Zawadi ya siri hutuliza hasira na zawadi ya kificho hutuliza ghadhabu kuu.
15 Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
Haki ikitendeka, huleta furaha kwa mwenye kutenda wema, lakini huleta hofu kubwa kwa watenda mabaya.
16 Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
Yule anayezurura kutoka kwenye njia ya ufahamu, atapumzika kwenye kusanyiko la wafu.
17 Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
Anayependa raha atakuwa masikini; anayependa divai na mafuta hawezi kuwa tajiri.
18 Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
Mtu mbaya ni fidia kwa yule atendaye haki, na mdanganyifu ni fidia kwa waaminifu.
19 Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
Bora kuishi jangwani kuliko kuishi pamoja na mwanamke ambaye huchochea sana ugomvi na malalamiko.
20 A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
Hazina yenye thamani na mafuta vipo nyumbani kwa mwenye busara, bali mtu mpumbavu huviharibu.
21 Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
Mtu atendaye haki na mwema -huyu mtu hupata uzima, haki na heshima.
22 Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
Mtu mwenye busara huupima mji wa mashujaa, na huiangusha ngome wanayoitumaini.
23 Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
Anayelinda kinywa chake na ulimi wake hujilinda mwenyewe na taabu.
24 Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
Mtu mwenye kiburi na maringo- “Dhihaka” ndilo jina lake - hutenda kwa majivuno na kujidai.
25 Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
Shauku ya mtu mvivu itamuua, maana mikono yake hukataa kufanya kazi.
26 Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
Kwa siku nzima hupatwa na uchu na uchu zaidi, lakini atendaye haki hutoa na wala hazuii.
27 Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
Sadaka ya mwovu ni chukizo; huwa ni chukizo zaidi anapoileta kwa nia mbaya.
28 Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
Shahidi wa uongo ataangamia, bali anayesikiliza ataongea kwa muda wote.
29 Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
Mtu mwovu huufanya uso wake kuwa mgumu, bali mtu mwadilifu ni thabiti juu ya njia zake.
30 Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
Hakuna hekima, hakuna ufahamu, na hakuna shauri linaloweza kusimama kinyume na Yehova.
31 Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
Farasi hutayarishwa kwa siku ya mapigano, lakini ushindi hupatikana kwa Yehova.