< Karin Magana 21 >
1 A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
Des Königs Herz ist in der Hand des HERRN wie Wasserbäche, und er neiget es, wohin er will.
2 Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
Einen jeglichen dünkt sein Weg recht sein; aber allein der HERR macht die Herzen gewiß.
3 Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
Wohl und recht tun ist dem HERRN lieber denn Opfer.
4 Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
Hoffärtige Augen und stolzer Mut und die Leuchte der Gottlosen ist Sünde.
5 Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
Die Anschläge eines Endelichen bringen Überfluß; wer aber allzu jach ist, wird mangeln.
6 Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
Wer Schätze sammelt mit Lügen, der wird fehlen und fallen unter die den Tod suchen.
7 Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
Der Gottlosen Rauben wird sie schrecken; denn sie wollten nicht tun, was recht war.
8 Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
Wer einen andern Weg gehet, der ist verkehrt; wer aber in seinem Befehl gehet, des Werk ist recht.
9 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Es ist besser wohnen im Winkel auf dem Dach, denn bei einem zänkischen Weibe in einem Hause beisammen.
10 Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
Die Seele des Gottlosen wünschet Arges und gönnet seinem Nächsten nichts.
11 Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
Wenn der Spötter gestraft wird, so werden die Albernen weise; und wenn man einen Weisen unterrichtet, so wird er vernünftig.
12 Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
Der Gerechte hält sich weislich gegen des Gottlosen Haus; aber die Gottlosen denken nur Schaden zu tun.
13 In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
Wer seine Ohren verstopft vor dem Schreien des Armen, der wird auch rufen und nicht erhöret werden.
14 Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
Eine heimliche Gabe stillet den Zorn und ein Geschenk im Schoß den heftigen Grimm.
15 Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
Es ist dem Gerechten eine Freude zu tun, was recht ist, aber eine Furcht den Übeltätern.
16 Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
Ein Mensch, der vom Wege der Klugheit irret, der wird bleiben in der Toten Gemeine.
17 Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
Wer gern in Wollust lebt, wird mangeln; und wer Wein und Öl liebet, wird nicht reich.
18 Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
Der Gottlose muß für den Gerechten gegeben werden und der Verächter für die Frommen.
19 Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
Es ist besser wohnen im wüsten Lande denn, bei einem zänkischen und zornigen Weibe.
20 A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
Im Hause des Weisen ist ein lieblicher Schatz und Öl aber ein Narr verschlemmt es.
21 Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
Wer der Barmherzigkeit und Güte nachjagt, der findet das Leben, Barmherzigkeit und Ehre.
22 Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
Ein Weiser gewinnet die Stadt der Starken und stürzet ihre Macht durch ihre Sicherheit.
23 Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
Wer seinen Mund und Zunge bewahret, der bewahret seine Seele vor Angst.
24 Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
Der stolz und vermessen ist, heißt ein loser Mensch, der im Zorn Stolz beweiset.
25 Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
Der Faule stirbt über seinem Wünschen; denn seine Hände wollen nichts tun.
26 Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
Er wünscht täglich; aber der Gerechte gibt und versagt nicht.
27 Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
Der Gottlosen Opfer ist ein Greuel; denn sie werden in Sünden geopfert.
28 Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
Ein lügenhaftiger Zeuge wird umkommen; aber wer gehorchet, den läßt man auch allezeit wiederum reden.
29 Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
Der Gottlose fährt mit dem Kopf hindurch; aber wer fromm ist, des Weg wird bestehen.
30 Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
Es hilft keine Weisheit, kein Verstand, kein Rat wider den HERRN.
31 Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
Rosse werden zum Streittage bereitet; aber der Sieg kommt vom HERRN.