< Karin Magana 21 >

1 A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
Le cœur du roi est un courant d’eau dans la main de l’Éternel; Il l’incline partout où il veut.
2 Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
Toutes les voies de l’homme sont droites à ses yeux; Mais celui qui pèse les cœurs, c’est l’Éternel.
3 Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
La pratique de la justice et de l’équité, Voilà ce que l’Éternel préfère aux sacrifices.
4 Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
Des regards hautains et un cœur qui s’enfle, Cette lampe des méchants, ce n’est que péché.
5 Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
Les projets de l’homme diligent ne mènent qu’à l’abondance, Mais celui qui agit avec précipitation n’arrive qu’à la disette.
6 Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
Des trésors acquis par une langue mensongère Sont une vanité fugitive et l’avant-coureur de la mort.
7 Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
La violence des méchants les emporte, Parce qu’ils refusent de faire ce qui est juste.
8 Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
Le coupable suit des voies détournées, Mais l’innocent agit avec droiture.
9 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Mieux vaut habiter à l’angle d’un toit, Que de partager la demeure d’une femme querelleuse.
10 Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
L’âme du méchant désire le mal; Son ami ne trouve pas grâce à ses yeux.
11 Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
Quand on châtie le moqueur, le sot devient sage; Et quand on instruit le sage, il accueille la science.
12 Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
Le juste considère la maison du méchant; L’Éternel précipite les méchants dans le malheur.
13 In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
Celui qui ferme son oreille au cri du pauvre Criera lui-même et n’aura point de réponse.
14 Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
Un don fait en secret apaise la colère, Et un présent fait en cachette calme une fureur violente.
15 Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
C’est une joie pour le juste de pratiquer la justice, Mais la ruine est pour ceux qui font le mal.
16 Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
L’homme qui s’écarte du chemin de la sagesse Reposera dans l’assemblée des morts.
17 Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
Celui qui aime la joie reste dans l’indigence; Celui qui aime le vin et l’huile ne s’enrichit pas.
18 Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
Le méchant sert de rançon pour le juste, Et le perfide pour les hommes droits.
19 Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
Mieux vaut habiter dans une terre déserte, Qu’avec une femme querelleuse et irritable.
20 A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
De précieux trésors et de l’huile sont dans la demeure du sage; Mais l’homme insensé les engloutit.
21 Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
Celui qui poursuit la justice et la bonté Trouve la vie, la justice et la gloire.
22 Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
Le sage monte dans la ville des héros, Et il abat la force qui lui donnait de l’assurance.
23 Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
Celui qui veille sur sa bouche et sur sa langue Préserve son âme des angoisses.
24 Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
L’orgueilleux, le hautain, s’appelle un moqueur; Il agit avec la fureur de l’arrogance.
25 Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
Les désirs du paresseux le tuent, Parce que ses mains refusent de travailler;
26 Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
Tout le jour il éprouve des désirs; Mais le juste donne sans parcimonie.
27 Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
Le sacrifice des méchants est quelque chose d’abominable; Combien plus quand ils l’offrent avec des pensées criminelles!
28 Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
Le témoin menteur périra, Mais l’homme qui écoute parlera toujours.
29 Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
Le méchant prend un air effronté, Mais l’homme droit affermit sa voie.
30 Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
Il n’y a ni sagesse, ni intelligence, Ni conseil, en face de l’Éternel.
31 Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
Le cheval est équipé pour le jour de la bataille, Mais la délivrance appartient à l’Éternel.

< Karin Magana 21 >