< Karin Magana 21 >
1 A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
As streams of water, So is the heart of the king in the hand of the LORD; He turneth it whithersoever he will.
2 Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
All the ways of a man are right in his own eyes; But the LORD weigheth the heart.
3 Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
To do justice and equity Is more acceptable to the LORD than sacrifice.
4 Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
The lofty look, the proud heart, The lamp of the wicked, is ruin.
5 Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
The plans of the diligent tend only to plenty; But the hasty hasteneth only to want.
6 Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
The getting of treasures by a false tongue Is the fleeting breath of them that seek death.
7 Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
The rapine of the wicked shall snatch them away, Because they refuse to do justice.
8 Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
The way of the guilty man is crooked; But he that is pure, his doings are right.
9 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
Better is it to dwell in a corner of the housetop Than with a brawling woman in a large house.
10 Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
The soul of the wicked longeth to do evil; His neighbor findeth no compassion in his eyes.
11 Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
When the scoffer is punished, the simple is made wise; When the wise man is taught, he receiveth knowledge.
12 Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
The righteous man hath regard to the house of the wicked; He casteth the wicked headlong into ruin.
13 In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
Whoso stoppeth his ears at the cry of the poor, He also shall cry aloud, but shall not be heard.
14 Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
A gift in secret pacifieth anger; And a present in the bosom, strong wrath.
15 Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
To do justice shall be joy to the righteous; But destruction is for them that do iniquity.
16 Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
A man who wandereth from the way of discretion Shall rest in the assembly of the dead.
17 Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
He that loveth pleasure will be a poor man; He that loveth wine and oil will not be rich.
18 Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
The wicked shall be a ransom for the righteous! And in the room of the upright shall be the transgressor.
19 Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
It is better to dwell in a desert land Than with a contentious and fretful woman.
20 A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
Precious treasure and oil are in the dwelling of the wise; But the foolish man swalloweth them up.
21 Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
He who followeth after righteousness and mercy Shall find life, prosperity, and honor.
22 Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
A wise man scaleth the city of the mighty, And bringeth down the strength in which it trusted.
23 Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
Whoso keepeth his mouth and his tongue Keepeth his soul from trouble.
24 Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
The proud and haughty, —scoffer is his name; He acteth with haughty arrogance.
25 Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
The desire of the sluggard will destroy him; For his hands refuse to labor.
26 Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
The covetous man coveteth all the day long; But the righteous man giveth, and doth not withhold.
27 Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
The sacrifice of the wicked is an abomination; How much more when he bringeth it with an evil design!
28 Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
A false witness shall perish; But a man that hearkeneth shall speak forever.
29 Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
The wicked man hardeneth his face; But the upright directeth his way.
30 Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
Wisdom is nothing, and understanding is nothing, And devices are nothing, against the LORD.
31 Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
The horse is prepared for the day of battle; But victory is from the LORD.