< Karin Magana 21 >
1 A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
The king's heart in the hand of Jehovah is [as] brooks of water: he turneth it whithersoever he will.
2 Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
Every way of a man is right in his own eyes; but Jehovah weigheth the hearts.
3 Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
To exercise justice and judgment is more acceptable to Jehovah than sacrifice.
4 Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
Lofty eyes, and a proud heart, the lamp of the wicked, is sin.
5 Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
The thoughts of the diligent [tend] only to plenteousness; but of every one that is hasty, only to want.
6 Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
The getting of treasures by a lying tongue is a fleeting breath of them that seek death.
7 Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
The devastation of the wicked sweepeth them away, because they refuse to do what is right.
8 Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
Very crooked is the way of a guilty man; but as for the pure, his work is upright.
9 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
It is better to dwell in a corner of the housetop, than with a contentious woman, and a house in common.
10 Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
The soul of the wicked desireth evil: his neighbour findeth no favour in his eyes.
11 Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
When the scorner is punished, the simple becometh wise; and when the wise is instructed, he receiveth knowledge.
12 Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
One that is righteous wisely considereth the house of the wicked: he overthroweth the wicked to [their] ruin.
13 In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
Whoso stoppeth his ears at the cry of the poor, he also himself shall cry, and shall not be heard.
14 Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
A gift in secret pacifieth anger; and a present in the bosom, vehement fury.
15 Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
It is joy to a righteous [man] to do what is right; but it is ruin for the workers of iniquity.
16 Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
The man that wandereth out of the way of wisdom shall abide in the congregation of the dead.
17 Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
He that loveth mirth shall be a poor man; he that loveth wine and oil shall not be rich.
18 Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
The wicked is a ransom for the righteous, and a treacherous [man] in the stead of the upright.
19 Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
It is better to dwell in a desert land. than with a contentious and irritable woman.
20 A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
There is costly store and oil in the dwelling of a wise [man]; but a foolish man swalloweth it up.
21 Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
He that followeth after righteousness and mercy findeth life, righteousness, and honour.
22 Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
A wise [man] scaleth the city of the mighty, and casteth down the strength of the confidence thereof.
23 Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
Whoso keepeth his mouth and his tongue keepeth his soul from troubles.
24 Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
Proud, arrogant, scorner is his name who dealeth in proud wrath.
25 Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
The desire of the sluggard killeth him; for his hands refuse to work:
26 Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
He coveteth greedily all the day long; but the righteous giveth and spareth not.
27 Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
The sacrifice of the wicked is abomination: how much more when they bring it with a wicked purpose!
28 Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
A lying witness shall perish; and a man that heareth shall speak constantly.
29 Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
A wicked man hardeneth his face; but as for the upright, he establisheth his way.
30 Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
There is no wisdom, nor understanding, nor counsel against Jehovah.
31 Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
The horse is prepared for the day of battle; but safety is of Jehovah.