< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
Xarab kixini rǝswa ⱪilar, Ⱨaraⱪ kixini ƣaljirlaxturar; Kimki uningƣa berilip ezip kǝtsǝ, ǝⱪilsizdur.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
Padixaⱨning ƣǝzipi xirning ⱨɵrkirixigǝ ohxax ⱪorⱪunqluⱪtur; Uning aqqiⱪini kǝltürgǝn, ɵz jeniƣa jaza qüxürǝr.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
Ɵzini majiradin neri ⱪilix kixining izzitidur; Biraⱪ ⱨǝrbir ǝhmǝⱪ ɵzini basalmas.
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
Ⱨurun adǝm ⱪixta yǝr ⱨǝydimǝs; Yiƣim waⱪtida yoⱪluⱪta ⱪelip axliⱪ tilǝr.
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
Kixining kɵnglidiki oy-niyǝtliri qongⱪur suƣa ohxaxtur; Yorutulƣan adǝm ularni tartip alalaydu.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
Ɵzini sadiⱪ dǝydiƣanlar kɵptur; Biraⱪ ixǝnqlik bir adǝmni kim tapalisun?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
Ⱨǝⱪⱪaniy adǝm diyanǝtlik yolda mangar; Uning pǝrzǝntlirigǝ bǝht-bǝrikǝt ⱪaldurular!
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
Padixaⱨ adalǝt tǝhtidǝ olturƣanda, Ⱨǝmmǝ yamanliⱪni kɵzi bilǝn ⱪoƣlaydu.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
Kim ɵzini gunaⱨdin tazilandim, Wijdanim paklandi, deyǝlǝydu?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
Ikki hil taraza texi, Ikki hil kürǝ ixlitix, Ohxaxla Pǝrwǝrdigarƣa yirginqliktur.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Ⱨǝtta bala ɵz hisliti bilǝn bilinǝr; Uning ⱪilƣanlirining pak, durus yaki ǝmǝsliki ⱨǝrikǝtliridin kɵrünüp turar.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
Kɵridiƣan kɵzni, anglaydiƣan ⱪulaⱪni, Ⱨǝr ikkisini Pǝrwǝrdigar yaratti.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
Uyⱪuƣa amraⱪ bolma, namratliⱪⱪa uqraysǝn; Kɵzüngni eqip oyƣaⱪ bol, nening mol bolar.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
Heridar mal alƣanda: «Naqar ikǝn, naqar ikǝn!» dǝp ⱪaⱪxaydu; Elip kǝtkǝndin keyin [«Esil nǝrsǝ, ǝrzan aldim» dǝp] mahtinidu.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Altun bar, lǝǝl-yaⱪutlarmu kɵptur; Biraⱪ bilimni beƣixliƣan lǝwlǝr nemidegǝn ⱪimmǝtlik gɵⱨǝrdur!
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Yatⱪa kepil bolƣan kixidin ⱪǝrzgǝ tonini tutup alƣin; Yat hotunƣa kapalǝt bǝrgǝn kixidin kapalǝt puli al.
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
Aldap erixkǝn tamaⱪ tatliⱪtur; Keyin, uning yegini xeƣil bolar.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Pilanlar mǝsliⱨǝt bilǝn bekitilǝr; Pixⱪan kɵrsǝtmǝ bilǝn jǝng ⱪilƣin.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
Gǝp toxuƣuqi sirlarni axkarilar; Xunga walaⱪtǝkkür bilǝn arilaxma.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
Kimki ata-anisini ⱨaⱪarǝt ⱪilsa, Uning qiriƣi zulmǝt ⱪarangƣusida ɵqǝr!
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
Tez erixkǝn miras ⱨaman bǝrikǝtlik bolmas.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
Yamanliⱪⱪa yamanliⱪ ⱪayturay demǝ; Pǝrwǝrdigarƣa tayinip küt, U dǝrdinggǝ yetǝr.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
Ikki hil taraza texi Pǝrwǝrdigarƣa yirginqliktur; Sahta ɵlqǝm ⱪǝt’iy yarimas.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
Insanning ⱨayatliⱪ ⱪǝdǝmlirini Pǝrwǝrdigar bǝlgilǝydu; Undaⱪta insan ɵz musapisini nǝdin bilsun?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Bir nǝrsisini yeniklik bilǝn «[Hudaƣa] atalƣan!» dǝp wǝdǝ berix, Ⱪǝsǝmlǝrdin keyin ikkilinip ⱪayta oylinix, Ɵz jenini ⱪiltaⱪⱪa qüxürgǝngǝ barawǝr.
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
Dana padixaⱨ yamanlarni topanni soruƣandǝk soruwetidu, Haman tǝpkǝndǝk tuluⱪ bilǝn yanjiwetǝr.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
Adǝmning roⱨ-wijdani — Pǝrwǝrdigarning qiriƣidur, U ⱪǝlbning ⱨǝrbir tǝglirini tǝkxürüp pǝrⱪ etǝr.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
Meⱨir-xǝpⱪǝt wǝ ⱨǝⱪiⱪǝt padixaⱨni saⱪlaydu; U meⱨir-xǝpⱪǝt bilǝnla ɵz tǝhtini mustǝⱨkǝmlǝydu.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
Yax yigitlǝrning ⱪawulluⱪi ularning pǝhridur; Ⱪerilarning izziti aⱪ qaqliridur.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Tǝrbiyǝ yariliri yamanliⱪni tazilap qiⱪirar, Tayaⱪ izliri iq-baƣirni taza ⱪilar.

< Karin Magana 20 >