< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
EL vino es escarnecedor, la cerveza alborotadora; y cualquiera que por ello errare, no será sabio.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
Como bramido de cachorro de león es el terror del rey: el que lo hace enfurecerse, peca [contra] su alma.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
Honra es del hombre dejarse de contienda: mas todo insensato se envolverá [en ella].
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
El perezoso no ara á causa del invierno; pedirá pues en la siega, y no [hallará].
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
[Como] aguas profundas es el consejo en el corazón del hombre: mas el hombre entendido lo alcanzará.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
Muchos hombres publican cada uno su liberalidad: mas hombre de verdad, ¿quién lo hallará?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
El justo que camina en su integridad, bienaventurados serán sus hijos después de él.
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
El rey que se sienta en el trono de juicio, con su mirar disipa todo mal.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
¿Quién podrá decir: Yo he limpiado mi corazón, limpio estoy de mi pecado?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
Doble pesa y doble medida, abominación son á Jehová ambas cosas.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Aun el muchacho es conocido por sus hechos, si su obra fuere limpia y recta.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
El oído que oye, y el ojo que ve, ambas cosas ha igualmente hecho Jehová.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
No ames el sueño, porque no te empobrezcas; abre tus ojos, [y] te hartarás de pan.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
El que compra dice: malo es, malo es: mas en apartándose, se alaba.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Hay oro y multitud de piedras preciosas: mas los labios sabios son vaso precioso.
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Quítale su ropa al que salió por fiador del extraño; y tómale prenda [al que fía] la extraña.
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
Sabroso es al hombre el pan de mentira; mas después su boca será llena de cascajo.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Los pensamientos con el consejo se ordenan: y con industria se hace la guerra.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
El que descubre el secreto, en chismes anda: no te entrometas, pues, con el que lisonjea con sus labios.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
El que maldice á su padre ó á su madre, su lámpara será apagada en oscuridad tenebrosa.
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
La herencia adquirida de priesa al principio, aun su postrimería no será bendita.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
No digas, yo me vengaré; espera á Jehová, y él te salvará.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
Abominación son á Jehová las pesas dobles; y el peso falso no es bueno.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
De Jehová son los pasos del hombre: ¿cómo pues entenderá el hombre su camino?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Lazo es al hombre el devorar lo santo, y andar pesquisando después de los votos.
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
El rey sabio esparce los impíos, y sobre ellos hace tornar la rueda.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
Candela de Jehová es el alma del hombre, que escudriña lo secreto del vientre.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
Misericordia y verdad guardan al rey; y con clemencia sustenta su trono.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
La gloria de los jóvenes es su fortaleza, y la hermosura de los viejos la vejez.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Las señales de las heridas son medicina para lo malo: y las llagas [llegan] á lo más secreto del vientre.

< Karin Magana 20 >