< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
El vino te transforma en un burlador, y el alcohol te vuelve agresivo. Si te dejas engañar por la bebida, eres un tonto.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
Cuando un rey se enoja en gran manera, se escuchará como un león rugiente. Quien haya causado su enojo corre el riesgo de ir a la muerte.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
Evitar el conflicto es hacer lo correcto. Pero los necios se apresuran a iniciar la discusión.
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
Los holgazanes no salen a sembrar cuando deberían. Por eso, cuando llega la cosecha, no tienen nada que recoger.
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
Descubrir lo que piensan los demás es como mirar en aguas profundas. Pero el que tiene entendimiento los conocerá.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
Muchos te dirán que son leales, pero ¿podrás hallar a una persona digna de confianza?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
El pueblo de Dios vive con honestidad. ¡Cuán felices son sus hijos si siguen tal ejemplo!
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
Cuando el rey se sienta a emitir un juicio, puede ver lo que no está bien.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
¿Quién puede decir: “Estoy seguro de que mi conciencia está limpia y estoy limpio de pecado”?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
El Señor aborrece el peso falso así como la medida falsa.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Hasta los niños revelan su carácter por lo que hacen, ya sean acciones buenas o malas.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
El Señor nos dio orejas para oír y ojos para ver.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
Si te gusta dormir, terminarás pobre. Levántate y trabaja, para que tengas qué comer.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
“Es basura”, dice el que compra, pero luego se jacta delante de otros de haber hecho un buen negocio.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Hay oro y muchas piedras preciosas. Pero hablar con sensatez es la joya más valiosa.
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Si alguno sirve como codeudor de un extranjero dando su abrigo como garantía de pago, asegúrate de tomarlo. ¡Toma todo lo que haya sido entregado como pago a favor de un extranjero!
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
La comida que es producto del fraude puede tener un dulce sabor, pero después verán sus bocas llenas de gravilla.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Con el consejo sabio, los planes son exitosos. Si vas a la guerra, asegúrate de tener la instrucción correcta.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
El chismoso anda de aquí para allá revelando secretos. Aléjate de aquellos que hablan mucho.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
Todo aquél que maldice a su padre o a su madre apaga su luz y terminará en oscuridad absoluta.
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
La riqueza rápida no te hará bien al final de cuentas.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
No digas: “Me pagarás por este mal que me has hecho”. Déjaselo al Señor, y él te ayudará.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
El Señor aborrece el peso incorrecto. No está bien usar peso falso.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
El Señor nos muestra el camino a seguir, ¿por qué habríamos de decidir nosotros mismos?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Es un error hacerle una promesa al Señor y luego arrepentirnos de lo que hemos prometido.
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
Un rey sabio separa a los malvados con un aventador y luego los castiga cuando hace el trillado.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
La luz del Señor brilla en la conciencia, revelando nuestros más profundos pensamientos.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
El amor fiel y la lealtad mantienen al rey a salvo. El amor fiel es el fundamento de su gobierno.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
Los jóvenes valoran su fuerza, pero los ancianos estiman más la sabiduría que viene con los años.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Los azotes espantan la maldad; los golpes limpian hasta adentro.

< Karin Magana 20 >