< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
O vinho é zombador, a bebida forte é causadora de alvoroços; e todo aquele que errar por causa deles não é sábio.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
O temor ao rei é como um rugido de leão; e quem se ira contra ele peca contra sua [própria] alma.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
É honroso ao homem terminar a disputa; mas todo tolo nela se envolve.
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
O preguiçoso não lavra no inverno; [por isso] ele mendigará durante a ceifa, pois nada terá.
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
O conselho no coração do homem [é como] águas profundas; mas o homem prudente [consegue] tirá-lo para fora.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
Muitos homens, cada um deles afirma ter bondade; porém o homem fiel, quem o encontrará?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
O justo caminha em sua integridade; bem-aventurados [serão] seus filhos depois dele.
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
O rei, ao se sentar no trono do juízo, com seus olhos dissipa todo mal.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
Quem poderá dizer: “Purifiquei meu coração; estou limpo de meu pecado”?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
Dois pesos e duas medidas, ambos são abominação ao SENHOR.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Até o jovem é conhecido pelas suas ações, se sua obra for pura e correta.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
O ouvido que ouve e o olho que vê, o SENHOR os fez ambos.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
Não ames ao sono, para que não empobreças; abre teus olhos, e te fartarás de pão.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
[Preço] ruim, [preço] ruim, diz o comprador; mas quando vai embora, então se gaba.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Há ouro, e muitos rubis; mas os lábios do conhecimento são joia preciosa.
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Toma a roupa daquele que fica por fiador de estranho; toma como penhor daquele [que fica por fiador] da estranha.
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
O pão da mentira é agradável ao homem; mas depois sua boca se encherá de pedregulhos.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Os planos são confirmados por meio do conselho; e com conselhos prudentes faze a guerra.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
Quem anda fofocando revela segredos; por isso não te envolvas com aquele que fala demais com seus lábios.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
Aquele que amaldiçoar a seu pai ou a sua mãe terá sua lâmpada apagada em trevas profundas.
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
A herança ganha apressadamente no princípio, seu fim não será abençoado.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
Não digas: Devolverei o mal; Espera pelo SENHOR, e ele te livrará.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
O SENHOR abomina pesos falsificados; e balanças enganosas não são boas.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
Os passos do homem pertencem ao SENHOR; como, pois, o homem entenderá seu caminho?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Armadilha ao homem é prometer precipitadamente algo como sagrado, e [somente] depois pensar na seriedade dos votos[ que fez].
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
O rei sábio espalha os perversos, e os atropela.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
O espírito humano é uma lâmpada do SENHOR, que examina todo o interior do ventre.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
A bondade e a fidelidade protegem o rei; e com bondade seu trono é sustentado.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
A beleza dos jovens é sua força; e a honra dos velhos é [seus] cabelos brancos.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Os golpes das feridas purificam os maus; como também as pancadas no interior do corpo.

< Karin Magana 20 >