< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Mwanangu, kama utayakubali maneno yangu na kuyaweka akiba maagizo yangu ndani mwako,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
kutega sikio lako kwenye hekima na kuweka moyo wako katika ufahamu,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
na kama ukiita busara na kuita kwa sauti ufahamu,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
na kama utaitafuta kama fedha na kuitafuta sana kama hazina iliyofichwa,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
ndipo utakapoelewa kumcha Bwana na kupata maarifa ya Mungu.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Kwa maana Bwana hutoa hekima, na kinywani mwake hutoka maarifa na ufahamu.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Anahifadhi ushindi kwa ajili ya mwadilifu, yeye ni ngao kwa wale wasio na lawama,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
kwa kuwa hulinda mwenendo wa mwenye haki na kuhifadhi njia ya waaminifu wake.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Ndipo utafahamu lipi lililo kweli na haki na sawa: yaani kila njia nzuri.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Kwa maana hekima itaingia moyoni mwako, nayo maarifa yataifurahisha nafsi yako.
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Busara itakuhifadhi na ufahamu utakulinda.
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Hekima itakuokoa kutoka njia za waovu, kutoka kwa watu ambao maneno yao yamepotoka,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
wale waachao mapito yaliyonyooka wakatembea katika njia za giza,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
wale wapendao kutenda mabaya na kufurahia upotovu wa ubaya,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
ambao mapito yao yamepotoka na ambao ni wapotovu katika njia zao.
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Itakuokoa pia kutokana na mwanamke kahaba, kutokana na mke aliyepotoka mwenye maneno ya kushawishi kutenda ubaya,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
aliyemwacha mwenzi wa ujana wake na kupuuza agano alilofanya mbele ya Mungu.
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Kwa maana nyumba yake huelekea kwenye kifo na mapito yake kwenye roho za waliokufa.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Hakuna yeyote aendaye kwake akarudi, au kufikia mapito ya uzima.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Hivyo utatembea katika njia za watu wema na kushikamana na mapito ya wenye haki.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Kwa maana wanyofu wataishi katika nchi, nao wasio na lawama watabakia ndani yake.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Bali waovu watakatiliwa mbali kutoka nchi, nao wasio waaminifu watangʼolewa kutoka humo.

< Karin Magana 2 >