< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Hijo mío, lleva mis palabras a tu corazón, guardando mis leyes en tu mente;
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
Para que tu oído preste atención a la sabiduría, y tu corazón se convierta en conocimiento.
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Verdaderamente, si clamas por el buen sentido, y tu pedido es por conocimiento;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
Si la estás buscando como plata, y buscándola como riqueza almacenada;
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Entonces el temor de Jehová será claro para ti, y el conocimiento de Dios será tuyo.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Porque el Señor da sabiduría; de su boca salen el conocimiento y la razón:
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Él tiene la salvación almacenada para los rectos, él es un pectoral para aquellos en quienes no hay maldad;
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
Vigila los caminos que son correctos, y cuida a los que le temen.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Entonces conocerás la justicia y la rectitud, y la conducta recta, incluso de todo buen camino.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Porque la sabiduría entrará en tu corazón, y el conocimiento agradará a tu alma;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Los propósitos sabios te cuidarán, y el conocimiento te mantendrá;
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Te da la salvación del hombre malo, de aquellos cuyas palabras son falsas;
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
Que dejan el camino de la justicia, para andar por caminos oscuros;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
Quienes se complacen en la maldad, y se complacen en los malos designios del pecador;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
Cuyos caminos no son rectos, y cuyos pasos se vuelven malvados:
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Para sacarte del poder de la mujer extraña, que dice palabras seductoras;
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
¿Quién es falsa con el marido de sus primeros años, y no tiene en cuenta el acuerdo con Dios?
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Porque su casa está en camino a la muerte; sus pasos descienden a las sombras:
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Los que van a ella no vuelven; sus pies no se mantienen en los caminos de la vida:
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
para que puedas seguir el camino de los hombres buenos, y seguir los pasos de los rectos.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Porque los rectos vivirán en la tierra, y los buenos la tendrán por heredad.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Pero los pecadores serán cortados de la tierra, y aquellos cuyos actos son falsos serán desarraigados.

< Karin Magana 2 >