< Karin Magana 2 >
1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
HIJO mío, si tomares mis palabras, y mis mandamientos guardares dentro de ti,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
Haciendo estar atento tu oído á la sabiduría; [si] inclinares tu corazón á la prudencia;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Si clamares á la inteligencia, y á la prudencia dieres tu voz;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
Si como á la plata la buscares, y la escudriñares como á tesoros;
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Entonces entenderás el temor de Jehová, y hallarás el conocimiento de Dios.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Porque Jehová da la sabiduría, y de su boca [viene] el conocimiento y la inteligencia.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
El provee de sólida sabiduría á los rectos: [es] escudo á los que caminan rectamente.
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
[Es] el que guarda las veredas del juicio, y preserva el camino de sus santos.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Entonces entenderás justicia, juicio, y equidad, y todo buen camino.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Cuando la sabiduría entrare en tu corazón, y la ciencia fuere dulce á tu alma,
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
El consejo te guardará, te preservará la inteligencia:
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Para librarte del mal camino, de los hombres que hablan perversidades;
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
Que dejan las veredas derechas, por andar en caminos tenebrosos;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
Que se alegran haciendo mal, que se huelgan en las perversidades del vicio;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
Cuyas veredas son torcidas, y torcidos sus caminos.
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Para librarte de la mujer extraña, de la ajena que halaga con sus palabras;
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
Que desampara el príncipe de su mocedad, y se olvida del pacto de su Dios.
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Por lo cual su casa está inclinada á la muerte, y sus veredas hacia los muertos:
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Todos los que á ella entraren, no volverán, ni tomarán las veredas de la vida.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Para que andes por el camino de los buenos, y guardes las veredas de los justos.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Porque los rectos habitarán la tierra, y los perfectos permanecerán en ella;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Mas los impíos serán cortados de la tierra, y los prevaricadores serán de ella desarraigados.