< Karin Magana 2 >
1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Hijo mío, si aceptas mis palabras, Y guardas mis mandamientos dentro de ti,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
Eres de oído atento a la sabiduría, E inclinas tu corazón a la inteligencia,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Si invocas a la prudencia, Y al entendimiento alzas tu voz,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
Si la procuras como a la plata, Y la rebuscas como a tesoros escondidos,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Entonces entenderás el temor a Yavé, Y hallarás el conocimiento de ʼElohim.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Porque Yavé da la sabiduría. De su boca procede la ciencia y la inteligencia.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Él atesora el acierto para los hombres rectos, Es escudo al que anda en integridad.
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
Es el que guarda las sendas de la justicia, Y preserva el camino de sus santos.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Entonces entenderás la justicia y el derecho, La equidad y todo buen camino.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Cuando la sabiduría entre en tu corazón Y el conocimiento sea dulce a tu alma,
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Te guardará la discreción. Te preservará la prudencia
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
Para librarte del camino malo Del hombre que habla cosas perversas,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
De los que abandonan los caminos rectos Para andar por sendas tenebrosas,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
De los que gozan haciendo el mal, Y se alegran en las perversidades del vicio,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
Cuyas sendas son tortuosas, Y sus caminos extraviados.
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Te librará de la mujer ajena, De la extraña que endulza sus palabras,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
Que abandona al compañero de su juventud Y olvida el Pacto de su ʼElohim.
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Su casa se inclina hacia la muerte, Sus sendas hacia el país de las sombras.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Cuantos entran en ella no regresan, Ni retoman los senderos de la vida.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Para que sigas el buen camino Y guardes los senderos del justo.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Porque los rectos vivirán en la tierra, Y los de limpio corazón permanecerán en ella.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Pero el perverso será cortado de la tierra, Y de ella serán desarraigados los transgresores.