< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Meu filho, se você receber minhas palavras, e guardar meus mandamentos dentro de você,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
so para voltar seus ouvidos à sabedoria, e aplique seu coração à compreensão;
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
sim, se você clamar por discernimento, e levante sua voz para a compreensão;
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
se você a procura como prata, e procurá-la como se fosse um tesouro escondido;
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
então você entenderá o medo de Yahweh, e encontrar o conhecimento de Deus.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Para Yahweh dá sabedoria. De sua boca sai o conhecimento e a compreensão.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Ele estabelece uma sólida sabedoria para os verticais. Ele é um escudo para aqueles que caminham em integridade,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
para que ele possa guardar os caminhos da justiça, e preservar o caminho de seus santos.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Então você entenderá a retidão e a justiça, equidade e todos os bons caminhos.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Pois a sabedoria entrará em seu coração. O conhecimento será agradável para sua alma.
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
A discrição irá cuidar de você. A compreensão o manterá,
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
para livrá-lo do caminho do mal, dos homens que falam coisas perversas,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
who abandona os caminhos da retidão, para caminhar nos caminhos da escuridão,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
que se regozijam de fazer o mal, e deleitar-se com a perversidade do mal,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
que são tortuosos em seus caminhos, e traiçoeiras em seus caminhos,
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
para entregá-lo da mulher estranha, mesmo da estrangeira que lisonjeia com suas palavras,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
que abandona a amiga de sua juventude, e esquece o pacto de seu Deus;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
para sua casa leva à morte, seus caminhos para os espíritos falecidos.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Nenhum outro que vá ao seu retorno, nem alcançam os caminhos da vida.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Por isso, caminhar no caminho dos homens bons, e manter os caminhos dos justos.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Pois os retos habitarão na terra. O perfeito permanecerá nele.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Mas os ímpios serão isolados da terra. Os traiçoeiros serão erradicados dela.

< Karin Magana 2 >