< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
O anake, naho iantofa’o o fivolakoo vaho akafi’o añ’ova’o ao o lilikoo,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
naho añilaña’o sofiñe ty hihitse, naho anokilaña’o troke ty hilala,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
naho kaihe’o ty fitsikarahañe, naho pazahe’o ty faharendrehañe
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
naho itsoeha’o hoe volafoty ikodebea’o hoe vara mikafitse:
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
Le ho rendre’o ty fañeveñañ’ am’ Iehovà vaho hitendreke ty fahafohinañe an’Andrianañahare.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Fa manolo-kihitse t’Iehovà boak’am-palie’e ao ty hilala naho ty faharendrehañe.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Añaja’e hihitse maharongatse amo vantañeo, fikalan-dRe amo mpañavelo an-kahitiañeo,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
arova’e o lalan-katòo, naho ambena’e ty lala’ o noro’eo.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Le ho fohi’o ty havantañañe naho ty hatò, naho ty hamiràñe, vaho ze lalañe soa;
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Hizilik’ añ’ova’o ao ty hihitse, naho hahafale ty tro’o ty hilala;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
Hañambeñ’ azo ty filieram-batañe, hijilova’ ty faharendrehañe;
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
hasita’e ami’ty lalan-karatiañe, amy t’indaty mivolam-bìlañe,
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
amo miveve boak’ amo lalan-kahitiañeoo, hijarabajaraba amo lalan-kaieñeo,
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
amo mirebek’ ami’ty hatsivokarañeo, naho mifale ami’ty hamengohan- karatiañeo,
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
ie mikelokeloke an-dia, vaho miridrike an-dalañe;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Hamotsots’azo ami’ty tsimirirañe, ami’ty karapilo mitsiriry an-drehake,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
i namorintseñe ty valin-katorà’ey, vaho mandikoke i fañinan’ Añahare’ey.
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
Migodroñe mb’am-pihomahañe ao ty akiba’e, minday mb’an-kavilasy ao o lala’eo;
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Le lia’e tsy mimpoly ze miheo mb’ama’e ao, tsy ho taka’e ka o lalan-kaveloñeo.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Aa le handenà’o ty lala’ o soao, naho hifahara’o o lala’ o vantañeoo.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Fa hitoboke amy taney o vañoñeo, vaho himoneñe ao o malio-tahiñeo;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Fe haitoañe amy taney o lo-tserekeo, vaho ho voroteñe o mpamañahio.

< Karin Magana 2 >