< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Fili mi, si susceperis sermones meos, et mandata mea absconderis penes te,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
ut audiat sapientiam auris tua: inclina cor tuum ad cognoscendam prudentiam.
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
Si enim sapientiam invocaveris, et inclinaveris cor tuum prudentiæ:
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
si quæsieris eam quasi pecuniam, et sicut thesauros effoderis illam:
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
tunc intelliges timorem Domini, et scientiam Dei invenies:
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
quia Dominus dat sapientiam: et ex ore eius prudentia, et scientia.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Custodiet rectorum salutem, et proteget gradientes simpliciter,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
servans semitas iustitiæ, et vias sanctorum custodiens.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Tunc intelliges iustitiam, et iudicium, et æquitatem, et omnem semitam bonam.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Si intraverit sapientia cor tuum, et scientia animæ tuæ placuerit:
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
consilium custodiet te, et prudentia servabit te,
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
ut eruaris a via mala, et ab homine, qui perversa loquitur:
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
qui relinquunt iter rectum, et ambulant per vias tenebrosas:
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
qui lætantur cum malefecerint, et exultant in rebus pessimis:
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
quorum viæ perversæ sunt, et infames gressus eorum.
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
Ut eruaris a muliere aliena, et ab extranea, quæ mollit sermones suos,
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
et relinquit Ducem pubertatis suæ,
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
et pacti Dei sui oblita est. Inclinata est enim ad mortem domus eius, et ad inferos semitæ ipsius. (questioned)
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Omnes, qui ingrediuntur ad eam, non revertentur, nec apprehendent semitas vitæ.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Ut ambules in via bona: et calles iustorum custodias.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Qui enim recti sunt, habitabunt in terra, et simplices permanebunt in ea.
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
Impii vero de terra perdentur: et qui inique agunt, auferentur ex ea.

< Karin Magana 2 >